• English
  • Business News
Sunday, May 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na Tantance Sakonnin Amurka Na Neman Tattaunawa A Kan Karin Haraji 

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Na Tantance Sakonnin Amurka Na Neman Tattaunawa A Kan Karin Haraji 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Jumma’a, ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ta bayyana cewa, a halin yanzu kasar tana nazarin halin da ake ciki, yayin da a baya-bayan nan Amurka take tuntuba ta hanyoyin da suka dace masu yawa, inda take bayyana muradin hawa teburin tattaunawa da kasar Sin kan batutuwan karin harajin kwastam.

Mai magana da yawun ma’aikatar cinikayyar Sin ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar cewa, kasar Sin tana nan a kan bakanta game da matsayin da ta dauka kan wannan batu, watau idan aka tilasta mata yaki kan lamarin, za ta sha damarar gwabzawa har sai ta ga abun da ya ture wa buzu nadi, kana idan aka zabi hawa teburin tattaunawa, to, kofarta a bude take.

  • FIRS Ta Umarci Bankuna Su Rufe Asusun Ajiyar Tara Harajin Da Ba Su Cika Ka’ida Ba
  • An Cafke Saurayi Bisa Zargin Yi Wa ‘Yar Budurwarsa Fyade A Bauchi

Sanarwar ta kuma ce, yakin karin harajin kwastam da na cinikayya, Amurka ce ita kadai ta kaddamar da yi, kuma idan har tana son a tattauna, tilas ne ta nuna da gaske take yi ta hanyar yin shirye-shirye da kuma daukar kwararan matakai, kamar su gyara kura-kuran da take tafkawa, da kuma soke karin harajin da ta yi ita kadai tsiga-tsiyau.

Ya yi nuni da cewa, kasar Sin ta lura da yadda Amurka ke ta faman magana a-kai-a-kai game da gyare-gyare kan matakan harajin da ta dauka. Jami’in ya ce, “A duk wata tattaunawa ko shawarwari da za a yi, idan har Amurka ba ta gyara kuskurenta na matakan harajin da ta dauka ita kadai ba, to hakan zai nuna rashin gaskiyarta, da kuma kara kawo cikas ga amincewa da juna.”

Mai magana da yawun ma’aikatar ya jaddada cewa, wayon da ake nunawa na abin da ake fada daban, wanda ake aikatawa daban, ko ma yunkurin amfani da tattaunawa don a fake da guzuma a harbi karsana da kuma cin zarafi ko shafa kashin kaji, ba zai yi tasiri a kan kasar Sin ba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Layukan Dogo Na Kasar Sin Sun Gudanar Da Sufurin Miliyoyin Fasinjoji A Ranar Farko Ta Hutun ‘Yan Kwadago

Next Post

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

Related

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

18 hours ago
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

19 hours ago
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari
Daga Birnin Sin

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

20 hours ago
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

22 hours ago
An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

22 hours ago
Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu
Daga Birnin Sin

Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu

23 hours ago
Next Post
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

LABARAI MASU NASABA

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

Tangarɗar Na’ura: JAMB Ta Sake Fitar Da Sakamakon Jarabawar UTME Ta 2025

May 25, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Ya Kuɓuta A Hannun ‘Yan Bindiga Bayan Shafe Kwanaki 8 Yana Gudu A Dajin Sokoto Da Neja

May 25, 2025
katsina

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 5 A Katsina

May 25, 2025
29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma

29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma

May 25, 2025
Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 

Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 

May 25, 2025
Warware Basussuka: WAEC DA NECO Sun Saki Sakamakon Ɗaliban Zamfara Na Shekara Biyar

Warware Basussuka: WAEC DA NECO Sun Saki Sakamakon Ɗaliban Zamfara Na Shekara Biyar

May 25, 2025
Shekaru 10, Kofuna 16 Kevin De Bruyne Ya Yi Bankwana Da Manchester City

Shekaru 10, Kofuna 16 Kevin De Bruyne Ya Yi Bankwana Da Manchester City

May 25, 2025
An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

May 24, 2025
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.