• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Gabatarwa Duniya Wata Sabuwar Hanyar Ci Gaba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Ta Gabatarwa Duniya Wata Sabuwar Hanyar Ci Gaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da safiyar yau Talata ne ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya kira taron manema labarai na ciki da wajen kasar Sin, a gefen taron majalisar wakilan jama’ar kasar karo na 14 dake wakana.

Minsitan ya ta amsa tambayoyi da dama da suka shafi kasar Sin da manufofi da dangantakarta da kasashen waje.
Dangane da zamanintar da kasar Sin, Qin Gang ya ce zamanantarwar ta Sin, ta samarwa duniya mafita dangane da kalubalen da take fuskanta. Tabbas nasarorirn da Sin ta samu sun shaida cewa, kowace kasa na da damar zabarwa kanta hanya mafi dacewa da ita. Hakika Sin ta zama abun misali ga sauran sassan duniya, domin ta bugi kirji ta yi abun da babu wata kasa da ta taba yi. Ta kasance kasa daya tilo da ta kai matakin da take yanzu, ba tare da mulkin mallaka ko danniya ba, lamarin da ya cancanci yabo ainun kuma ya dace a yi koyi da shi. Ta kuma nuna wa duniya wata tsaftattaciyar hanyar samun ci gaba mai dorewa.

Ya kuma amsa tambaya game da dangantakar Sin da Amurka. Yana mai cewa, ya kamata Amurka da Sin su hada hannu wajen mayar da dangantakarsu bisa turba. Kamar yadda ministan ya fada, idan har Amurka ta ci gaba da takala, to za ta haifar da fito-na-fito da tsamin dangantaka.

Lallai ya kamata Amurka ta gane cewa, babu wani matsin lamba ko yada jita-jita da zai kai ga dakile ci gaban kasar Sin, domin salonta na raya kai, ya fi mayar da hankali ne kan albarkatunta na cikin gida, kuma tubalin ci gabanta na da karfi, don haka da wuya a iya dakile ci gaban da ta samu. Haka kuma, kasuwar kasar Sin mai bude kofa, dama ce ga kamfanonin Amurkar da ma na sauran sassan duniya, don haka, bita da kulli ba zai kai Amurka ga cimma burinta na dakile Sin ba, sai ma dai ta dakile ci gaban kamfanoninta.

Dangane da dangantakar Sin da Rasha da ma rikicin Ukraine, ya ce dangantakar Rasha da Sin ba ta zama barazana ga kowa. Dangantaka ce ta mutuntawa da moriyar juna. A ganina irin dangantakar Sin da Rasha, ita ake bukata tsakanin kasa da kasa musamman ma manyan kasashe, domin zama abun misali. Dangantaka ce irin ta girmama juna da mutunci, wadda babu katsalandan ko neman ganin faduwar wani banagre.

Labarai Masu Nasaba

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Game da rikicin Ukraine kuwa, ministan ya ce bai kyautu a yi wa Sin barazana ko kakaba mata takunkumi ba. Sam neman da ake yi na shafawa Sin bakin fenti dangane da rikicin bai dace ba, domin ta kasance mai kira da yin sulhu da tsagaita bude wuta. Haka kuma ba mu taba jin inda aka ce Sin din ta bayar da gudunmuwar wani abu ga wani bangare a rikicin ba.

Wannan shi ne halin dattako da sanin ya kamata, kuma haka ya kamata duk wata babbar kasa, da take neman zaman lafiyar duniya da gaske ta yi. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Shugaban Kasa: Gamayyar Kungiyoyi 18 Sun Yi Zanga-zangar Neman Shugaban INEC Ya Sauka Daga Mukaminsa

Next Post

An Gabatar Da Shirin Sake Fasalin Cibiyoyin Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Don Tattaunawa

Related

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya
Daga Birnin Sin

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

15 hours ago
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

16 hours ago
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 
Daga Birnin Sin

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

16 hours ago
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya
Daga Birnin Sin

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

19 hours ago
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

19 hours ago
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

21 hours ago
Next Post
An Gabatar Da Shirin Sake Fasalin Cibiyoyin Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Don Tattaunawa

An Gabatar Da Shirin Sake Fasalin Cibiyoyin Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Don Tattaunawa

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.