• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Gabatarwa Duniya Wata Sabuwar Hanyar Ci Gaba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Ta Gabatarwa Duniya Wata Sabuwar Hanyar Ci Gaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da safiyar yau Talata ne ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya kira taron manema labarai na ciki da wajen kasar Sin, a gefen taron majalisar wakilan jama’ar kasar karo na 14 dake wakana.

Minsitan ya ta amsa tambayoyi da dama da suka shafi kasar Sin da manufofi da dangantakarta da kasashen waje.
Dangane da zamanintar da kasar Sin, Qin Gang ya ce zamanantarwar ta Sin, ta samarwa duniya mafita dangane da kalubalen da take fuskanta. Tabbas nasarorirn da Sin ta samu sun shaida cewa, kowace kasa na da damar zabarwa kanta hanya mafi dacewa da ita. Hakika Sin ta zama abun misali ga sauran sassan duniya, domin ta bugi kirji ta yi abun da babu wata kasa da ta taba yi. Ta kasance kasa daya tilo da ta kai matakin da take yanzu, ba tare da mulkin mallaka ko danniya ba, lamarin da ya cancanci yabo ainun kuma ya dace a yi koyi da shi. Ta kuma nuna wa duniya wata tsaftattaciyar hanyar samun ci gaba mai dorewa.

Ya kuma amsa tambaya game da dangantakar Sin da Amurka. Yana mai cewa, ya kamata Amurka da Sin su hada hannu wajen mayar da dangantakarsu bisa turba. Kamar yadda ministan ya fada, idan har Amurka ta ci gaba da takala, to za ta haifar da fito-na-fito da tsamin dangantaka.

Lallai ya kamata Amurka ta gane cewa, babu wani matsin lamba ko yada jita-jita da zai kai ga dakile ci gaban kasar Sin, domin salonta na raya kai, ya fi mayar da hankali ne kan albarkatunta na cikin gida, kuma tubalin ci gabanta na da karfi, don haka da wuya a iya dakile ci gaban da ta samu. Haka kuma, kasuwar kasar Sin mai bude kofa, dama ce ga kamfanonin Amurkar da ma na sauran sassan duniya, don haka, bita da kulli ba zai kai Amurka ga cimma burinta na dakile Sin ba, sai ma dai ta dakile ci gaban kamfanoninta.

Dangane da dangantakar Sin da Rasha da ma rikicin Ukraine, ya ce dangantakar Rasha da Sin ba ta zama barazana ga kowa. Dangantaka ce ta mutuntawa da moriyar juna. A ganina irin dangantakar Sin da Rasha, ita ake bukata tsakanin kasa da kasa musamman ma manyan kasashe, domin zama abun misali. Dangantaka ce irin ta girmama juna da mutunci, wadda babu katsalandan ko neman ganin faduwar wani banagre.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Game da rikicin Ukraine kuwa, ministan ya ce bai kyautu a yi wa Sin barazana ko kakaba mata takunkumi ba. Sam neman da ake yi na shafawa Sin bakin fenti dangane da rikicin bai dace ba, domin ta kasance mai kira da yin sulhu da tsagaita bude wuta. Haka kuma ba mu taba jin inda aka ce Sin din ta bayar da gudunmuwar wani abu ga wani bangare a rikicin ba.

Wannan shi ne halin dattako da sanin ya kamata, kuma haka ya kamata duk wata babbar kasa, da take neman zaman lafiyar duniya da gaske ta yi. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Shugaban Kasa: Gamayyar Kungiyoyi 18 Sun Yi Zanga-zangar Neman Shugaban INEC Ya Sauka Daga Mukaminsa

Next Post

An Gabatar Da Shirin Sake Fasalin Cibiyoyin Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Don Tattaunawa

Related

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

3 hours ago
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya
Daga Birnin Sin

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

4 hours ago
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

5 hours ago
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

6 hours ago
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

7 hours ago
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

8 hours ago
Next Post
An Gabatar Da Shirin Sake Fasalin Cibiyoyin Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Don Tattaunawa

An Gabatar Da Shirin Sake Fasalin Cibiyoyin Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Don Tattaunawa

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga KwaÉ—ayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga KwaÉ—ayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.