• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Gabatarwa Duniya Wata Sabuwar Hanyar Ci Gaba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Ta Gabatarwa Duniya Wata Sabuwar Hanyar Ci Gaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da safiyar yau Talata ne ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya kira taron manema labarai na ciki da wajen kasar Sin, a gefen taron majalisar wakilan jama’ar kasar karo na 14 dake wakana.

Minsitan ya ta amsa tambayoyi da dama da suka shafi kasar Sin da manufofi da dangantakarta da kasashen waje.
Dangane da zamanintar da kasar Sin, Qin Gang ya ce zamanantarwar ta Sin, ta samarwa duniya mafita dangane da kalubalen da take fuskanta. Tabbas nasarorirn da Sin ta samu sun shaida cewa, kowace kasa na da damar zabarwa kanta hanya mafi dacewa da ita. Hakika Sin ta zama abun misali ga sauran sassan duniya, domin ta bugi kirji ta yi abun da babu wata kasa da ta taba yi. Ta kasance kasa daya tilo da ta kai matakin da take yanzu, ba tare da mulkin mallaka ko danniya ba, lamarin da ya cancanci yabo ainun kuma ya dace a yi koyi da shi. Ta kuma nuna wa duniya wata tsaftattaciyar hanyar samun ci gaba mai dorewa.

Ya kuma amsa tambaya game da dangantakar Sin da Amurka. Yana mai cewa, ya kamata Amurka da Sin su hada hannu wajen mayar da dangantakarsu bisa turba. Kamar yadda ministan ya fada, idan har Amurka ta ci gaba da takala, to za ta haifar da fito-na-fito da tsamin dangantaka.

Lallai ya kamata Amurka ta gane cewa, babu wani matsin lamba ko yada jita-jita da zai kai ga dakile ci gaban kasar Sin, domin salonta na raya kai, ya fi mayar da hankali ne kan albarkatunta na cikin gida, kuma tubalin ci gabanta na da karfi, don haka da wuya a iya dakile ci gaban da ta samu. Haka kuma, kasuwar kasar Sin mai bude kofa, dama ce ga kamfanonin Amurkar da ma na sauran sassan duniya, don haka, bita da kulli ba zai kai Amurka ga cimma burinta na dakile Sin ba, sai ma dai ta dakile ci gaban kamfanoninta.

Dangane da dangantakar Sin da Rasha da ma rikicin Ukraine, ya ce dangantakar Rasha da Sin ba ta zama barazana ga kowa. Dangantaka ce ta mutuntawa da moriyar juna. A ganina irin dangantakar Sin da Rasha, ita ake bukata tsakanin kasa da kasa musamman ma manyan kasashe, domin zama abun misali. Dangantaka ce irin ta girmama juna da mutunci, wadda babu katsalandan ko neman ganin faduwar wani banagre.

Labarai Masu Nasaba

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Game da rikicin Ukraine kuwa, ministan ya ce bai kyautu a yi wa Sin barazana ko kakaba mata takunkumi ba. Sam neman da ake yi na shafawa Sin bakin fenti dangane da rikicin bai dace ba, domin ta kasance mai kira da yin sulhu da tsagaita bude wuta. Haka kuma ba mu taba jin inda aka ce Sin din ta bayar da gudunmuwar wani abu ga wani bangare a rikicin ba.

Wannan shi ne halin dattako da sanin ya kamata, kuma haka ya kamata duk wata babbar kasa, da take neman zaman lafiyar duniya da gaske ta yi. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Shugaban Kasa: Gamayyar Kungiyoyi 18 Sun Yi Zanga-zangar Neman Shugaban INEC Ya Sauka Daga Mukaminsa

Next Post

An Gabatar Da Shirin Sake Fasalin Cibiyoyin Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Don Tattaunawa

Related

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

2 hours ago
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
Daga Birnin Sin

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

3 hours ago
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

4 hours ago
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing
Daga Birnin Sin

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

5 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

23 hours ago
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

1 day ago
Next Post
An Gabatar Da Shirin Sake Fasalin Cibiyoyin Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Don Tattaunawa

An Gabatar Da Shirin Sake Fasalin Cibiyoyin Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Don Tattaunawa

LABARAI MASU NASABA

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya KarÉ“i Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya KarÉ“i Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 

August 2, 2025
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

August 2, 2025
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.