ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Gabatarwa Duniya Wata Sabuwar Hanyar Ci Gaba

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Da safiyar yau Talata ne ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya kira taron manema labarai na ciki da wajen kasar Sin, a gefen taron majalisar wakilan jama’ar kasar karo na 14 dake wakana.

Minsitan ya ta amsa tambayoyi da dama da suka shafi kasar Sin da manufofi da dangantakarta da kasashen waje.
Dangane da zamanintar da kasar Sin, Qin Gang ya ce zamanantarwar ta Sin, ta samarwa duniya mafita dangane da kalubalen da take fuskanta. Tabbas nasarorirn da Sin ta samu sun shaida cewa, kowace kasa na da damar zabarwa kanta hanya mafi dacewa da ita. Hakika Sin ta zama abun misali ga sauran sassan duniya, domin ta bugi kirji ta yi abun da babu wata kasa da ta taba yi. Ta kasance kasa daya tilo da ta kai matakin da take yanzu, ba tare da mulkin mallaka ko danniya ba, lamarin da ya cancanci yabo ainun kuma ya dace a yi koyi da shi. Ta kuma nuna wa duniya wata tsaftattaciyar hanyar samun ci gaba mai dorewa.

Ya kuma amsa tambaya game da dangantakar Sin da Amurka. Yana mai cewa, ya kamata Amurka da Sin su hada hannu wajen mayar da dangantakarsu bisa turba. Kamar yadda ministan ya fada, idan har Amurka ta ci gaba da takala, to za ta haifar da fito-na-fito da tsamin dangantaka.

ADVERTISEMENT

Lallai ya kamata Amurka ta gane cewa, babu wani matsin lamba ko yada jita-jita da zai kai ga dakile ci gaban kasar Sin, domin salonta na raya kai, ya fi mayar da hankali ne kan albarkatunta na cikin gida, kuma tubalin ci gabanta na da karfi, don haka da wuya a iya dakile ci gaban da ta samu. Haka kuma, kasuwar kasar Sin mai bude kofa, dama ce ga kamfanonin Amurkar da ma na sauran sassan duniya, don haka, bita da kulli ba zai kai Amurka ga cimma burinta na dakile Sin ba, sai ma dai ta dakile ci gaban kamfanoninta.

Dangane da dangantakar Sin da Rasha da ma rikicin Ukraine, ya ce dangantakar Rasha da Sin ba ta zama barazana ga kowa. Dangantaka ce ta mutuntawa da moriyar juna. A ganina irin dangantakar Sin da Rasha, ita ake bukata tsakanin kasa da kasa musamman ma manyan kasashe, domin zama abun misali. Dangantaka ce irin ta girmama juna da mutunci, wadda babu katsalandan ko neman ganin faduwar wani banagre.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Game da rikicin Ukraine kuwa, ministan ya ce bai kyautu a yi wa Sin barazana ko kakaba mata takunkumi ba. Sam neman da ake yi na shafawa Sin bakin fenti dangane da rikicin bai dace ba, domin ta kasance mai kira da yin sulhu da tsagaita bude wuta. Haka kuma ba mu taba jin inda aka ce Sin din ta bayar da gudunmuwar wani abu ga wani bangare a rikicin ba.

Wannan shi ne halin dattako da sanin ya kamata, kuma haka ya kamata duk wata babbar kasa, da take neman zaman lafiyar duniya da gaske ta yi. (Fa’iza Mustapha)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
An Gabatar Da Shirin Sake Fasalin Cibiyoyin Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Don Tattaunawa

An Gabatar Da Shirin Sake Fasalin Cibiyoyin Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Don Tattaunawa

LABARAI MASU NASABA

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.