• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Kasance Ja Gaba Wajen Lalubowa Duniya Sabbin Damarmakin Ci Gaba

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An kammala taron shekara-shekara na dandalin tattaunawa kan ci gaban kasar Sin a jiya Litinin, inda mahalarta ke ganin  cewa ta hanyar ci gaba mai inganci da bude kofarta, ba kokarin samun ci gaba bisa kuzarinta da boyayyen karfinta kadai Sin ke yi ba, har ma da taka rawar gani wajen gaggauta ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya.

A ko da yaushe Sin kan furta cewa, gabanta ba barazana ba ce, dama ce. A ganina, tabbas haka batun yake domin duk wani ci gaban da Sin take samu, tana gabatar da shi ga duniya domin samar da sabbin dabaru.

  • Sin Ta Taka Rawar Gani Ga Bunkasuwar Tattalin Arzikin Duniya
  • Kasar Sin Na Maraba Da Abokai ‘Yan Kasuwa Daga Kasashe Daban Daban Da Su Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar 

Kamar yadda a kullum kasar ke zama abun misali ko koyi ga sauran kasashe, duk wani ci gaban da Sin ta samu, zai kasance tamkar zaburarwa ne ga kasashen duniya na son koyi da ita domin kada a bar su a baya. Za mu iya cewa, kasar Sin ta kasance jagora kuma ja gaba, wajen lalubowa duniya sabbin hanyoyin samun ci gaba cikin lumana da ma shawo kan matsaloli.

Ci gaban Sin zai ci gaba da kasancewa tabbaci ga sauran kasashe musamman kasashe masu tasowa cewa, su ma za su iya samun ci gaban tattalin arziki da kyautatuwar zamantakewa kamar na Sin, idan suka nace, suka kuma zabarwa kansu manufofin da suka dace da yanayinsu, kana suka sanya kishin kasa da ruhin sadaukarwa a zukatansu kamar yadda Sin ta yi.

Mun ga yadda al’amura suka tsaya cik a lokacin da annobar COVID-19 ta aukawa kasar Sin. Mun shaida yadda aka samu tsaikon samun kayayyaki da hauhawar farashinsu saboda tasirin COVID-19 a kasar Sin. To kamar yadda aka ga mummunan tasiri a wancan lokaci, haka ci gaban kasar Sin zai haifar da kyakkyawan tasiri ga duniya.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Idan muka duba bangarori kamar na fasahohin zamani, kowa ya san kasar Sin ce ja gaba a wannan fanni, kuma tana samar da sabbin fasahohi kusan kullum a bangarori daban daban da suka shafi rayuwar jama’a da ayyukansu. Misali yadda take ingantawa da zamanintar da aikin gona, abu ne da zai taka rawar gani wajen samar da wadatar abinci a duniya. Motoci masu amfani da lantarki da Sin take samarwa, za su yi matukar amfani wajen rage dogaro da man fetur, da rage dumamar yanayi don samar da kyakkyawan muhallin rayuwa ga bil adama. Haka ma, bude kofarta da take kara yi, wata dama ce ga kamfanonin kasashen waje na cin gajiyar ci gaban kasar da babbar kasuwar da take da ita.

Don haka abun yi shi ne, kasashen dake neman ci gaba da gaske, su daura damara, su shirya, domin kasar Sin za ta lalubo musu sabbin hanyoyin da za su kara samun alfanu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Taka Rawar Gani Ga Bunkasuwar Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Hadin Gwiwar Shawarar BRI Tsakanin Habasha Da Sin Zai Kara Bunkasa Rayuwar Al’ummun Habasha

Related

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

13 hours ago
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana
Daga Birnin Sin

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

14 hours ago
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
Daga Birnin Sin

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

15 hours ago
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

16 hours ago
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu
Daga Birnin Sin

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

2 days ago
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

2 days ago
Next Post
BRI

Hadin Gwiwar Shawarar BRI Tsakanin Habasha Da Sin Zai Kara Bunkasa Rayuwar Al’ummun Habasha

LABARAI MASU NASABA

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.