ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Kasance Ja Gaba Wajen Lalubowa Duniya Sabbin Damarmakin Ci Gaba

by CGTN Hausa
2 years ago
sin

An kammala taron shekara-shekara na dandalin tattaunawa kan ci gaban kasar Sin a jiya Litinin, inda mahalarta ke ganin  cewa ta hanyar ci gaba mai inganci da bude kofarta, ba kokarin samun ci gaba bisa kuzarinta da boyayyen karfinta kadai Sin ke yi ba, har ma da taka rawar gani wajen gaggauta ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya.

A ko da yaushe Sin kan furta cewa, gabanta ba barazana ba ce, dama ce. A ganina, tabbas haka batun yake domin duk wani ci gaban da Sin take samu, tana gabatar da shi ga duniya domin samar da sabbin dabaru.

  • Sin Ta Taka Rawar Gani Ga Bunkasuwar Tattalin Arzikin Duniya
  • Kasar Sin Na Maraba Da Abokai ‘Yan Kasuwa Daga Kasashe Daban Daban Da Su Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar 

Kamar yadda a kullum kasar ke zama abun misali ko koyi ga sauran kasashe, duk wani ci gaban da Sin ta samu, zai kasance tamkar zaburarwa ne ga kasashen duniya na son koyi da ita domin kada a bar su a baya. Za mu iya cewa, kasar Sin ta kasance jagora kuma ja gaba, wajen lalubowa duniya sabbin hanyoyin samun ci gaba cikin lumana da ma shawo kan matsaloli.

ADVERTISEMENT

Ci gaban Sin zai ci gaba da kasancewa tabbaci ga sauran kasashe musamman kasashe masu tasowa cewa, su ma za su iya samun ci gaban tattalin arziki da kyautatuwar zamantakewa kamar na Sin, idan suka nace, suka kuma zabarwa kansu manufofin da suka dace da yanayinsu, kana suka sanya kishin kasa da ruhin sadaukarwa a zukatansu kamar yadda Sin ta yi.

Mun ga yadda al’amura suka tsaya cik a lokacin da annobar COVID-19 ta aukawa kasar Sin. Mun shaida yadda aka samu tsaikon samun kayayyaki da hauhawar farashinsu saboda tasirin COVID-19 a kasar Sin. To kamar yadda aka ga mummunan tasiri a wancan lokaci, haka ci gaban kasar Sin zai haifar da kyakkyawan tasiri ga duniya.

LABARAI MASU NASABA

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Idan muka duba bangarori kamar na fasahohin zamani, kowa ya san kasar Sin ce ja gaba a wannan fanni, kuma tana samar da sabbin fasahohi kusan kullum a bangarori daban daban da suka shafi rayuwar jama’a da ayyukansu. Misali yadda take ingantawa da zamanintar da aikin gona, abu ne da zai taka rawar gani wajen samar da wadatar abinci a duniya. Motoci masu amfani da lantarki da Sin take samarwa, za su yi matukar amfani wajen rage dogaro da man fetur, da rage dumamar yanayi don samar da kyakkyawan muhallin rayuwa ga bil adama. Haka ma, bude kofarta da take kara yi, wata dama ce ga kamfanonin kasashen waje na cin gajiyar ci gaban kasar da babbar kasuwar da take da ita.

Don haka abun yi shi ne, kasashen dake neman ci gaba da gaske, su daura damara, su shirya, domin kasar Sin za ta lalubo musu sabbin hanyoyin da za su kara samun alfanu.

sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa
Daga Birnin Sin

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026
Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

September 9, 2026
Next Post
BRI

Hadin Gwiwar Shawarar BRI Tsakanin Habasha Da Sin Zai Kara Bunkasa Rayuwar Al’ummun Habasha

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

September 9, 2026
Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.