• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Samu Karbuwa A Afirka Ta Hanyar Samar Da Abubuwa Masu Amfani

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya-bayan nan ne jaridar “Business Day” ta Najeriya, da sauran kafofin watsa labaru na kasar, suka ba da rahoton cewa, kamfanonin harhada magunguna na kasar Sin da ta Najeriya na shirin yin hadin gwiwa, don gina wata masana’antar harhada magunguna da darajarta ta kai dalar Amurka miliyan 100 a jihar Legas.

 

Akwai wasu muhimman batutuwa game da wannan hadin gwiwa: Na farko, kamfanonin kasar Sin da ke halartar aikin sun kware wajen samar da magungunan cutar kanjamau, kuma manufar gina masana’antar harhada magunguna ita ce inganta dogaro da kai a Najeriya ta fuskar aikin kiwon lafiya, musamman ma a fannin samar da magungunan hana yaduwar cutar kanjamau.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Ke Lebanon 
  • Shugaba Tinubu Ya Sake Aika Tallafin Buhun Shinkafa 18,500 Kebbi

Abu na biyu kuma shi ne, an samar da shirin kafa wannan masana’anta ne bayan da kamfanonin harhada magunguna na kasar Amurka da na Turai, irin su GSK da Sanofi, suka janye daga Najeriya kwanan nan. Bisa la’akari da hauhawar farashin kayayyaki, da karancin wutar lantarki, da tabarbarewar yanayin zuba jari, da sauran matsalolin da Najeriya ta fuskanta a shekarun nan, kamfanonin harhada magunguna na yammacin duniya sun zabi janye jiki daga kasar, duk da cewa yin hakan ya kara ta’azzara matsalar karancin magunguna a Najeriya.

 

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Daga wannan kwatance na “wani bangare ya fita waje, yayin da wani ya shiga ciki”, za mu iya fahimtar wani abu mai zurfi, wato dalilin da ya sa kasashen Afirka ke maraba da goyon bayan kasar Sin shi ne:

Na farko, kamfanonin kasar Sin sun dace da muhallin Afirka.

 

Lokacin da kamfanonin kasashen Yamma suka kasa jurewa kuma suka fice daya bayan daya, a nasu bangare kamfanonin kasar Sin na shigowa. Wannan ya nuna karfin kamfanonin kasar Sin, musamman ma a fannonin takaita kudin da ake kashewa, da kuma tinkarar hadari. Wannan ne ya sa sau da dama da kasashen Afirka ke matukar bukatar samun jari, Sinawa ne kadai ke iya ba su goyon baya.

 

Na biyu, Sinawa na da niyyar biyan bukatun jama’ar kasashen Afirka.

Alkaluma daga Majalisar Dinkin Duniya da hukumomin Najeriya sun nuna cewa, a yanzu haka akwai mutane miliyan 2 da suka kamu da cutar kanjamau a Najeriya, tare da samun sabbin masu kamuwa da cutar 1,400 a duk mako, sannan cutar ta sa yara miliyan 1.2 zama marayu. Saboda haka, yadda ake taimakawa Najeriya samun karfin samar da magungunan cutar kanjamau, wani mataki ne na adalci, dake samar da taimakon gaggawa ga al’ummar kasar, musamman ma marasa galihu. Yin hakan ya dace da tunanin gargajiya na Sinawa, na mai da adalci a gaban moriya.

 

Na uku, kasar Sin tana kokarin cika alkawuran da ta dauka.

A gun taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka da aka yi a birnin Beijing na Sin a watan da ya gabata, kasar Sin ta gabatar da “Ayyuka 10 na hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka don tabbatar da zamanantarwa”, ciki har da “Aikin hadin gwiwa a fannin lafiya”, wanda ya kunshi sa kaimi ga kamfanonin kasar Sin don su zuba jari ga harkar samar da magunguna a Afirka, da inganta bangaren kiwon lafiyar jama’a a kasashen Afirka, da dai sauransu. Babu shakka, wannan aiki na gina masana’antar harhada magunguna a Najeriya, mataki ne na aiwatar da manufofin da aka gabatar a taron kolin da ya gudana.

 

Idan aka kwatanta da dimbin ayyukan hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, wannan aiki na kafa masana’antar harhada magunguna ba wani aiki mai matukar muhimmanci ba ne. Amma duk da haka, an tabbatar da kimar kasar Sin a Afirka ta hanyar gudanar da ire-iren wadannan ayyuka. Suna iya zama wata masana’antar harhada magunguna, ko madatsar ruwa, da layin dogo, da tashar samar da wutar lantarki ta zafin rana, da dai sauransu. Wato abubuwa ne masu amfani da za su taimaki al’ummar kasashen Afirka wajen magance matsaloli, da kuma samar musu da fa’ida ta zahiri. Dalilin da ya sa kasar Sin ke daukar wadannan matakai, shi ne tunaninta na hadin gwiwa da kasashen Afirka ta hanyar nuna gaskiya, da neman samar da hakikanin sakamako, da tabbatar da zumunta da sahihanci. Wannan tunani ya sa ake samun dangantakar hadin gwiwa mai amfanin juna tsakanin Sin da Afirka, har ma ya sa zumuntar dake tsakaninsu karfafa a kai a kai. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaNDLEASin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Tinubu Ya Sake Aika Tallafin Buhun Shinkafa 18,500 Kebbi

Next Post

Wakilin Sin Ya Bukaci A Kyautata Tsarin Duniya Da Gyara Rashin Adalci Da Aka Yi Wa Afirka

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

4 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

5 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

6 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

7 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

8 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

18 hours ago
Next Post
Wakilin Sin Ya Bukaci A Kyautata Tsarin Duniya Da Gyara Rashin Adalci Da Aka Yi Wa Afirka

Wakilin Sin Ya Bukaci A Kyautata Tsarin Duniya Da Gyara Rashin Adalci Da Aka Yi Wa Afirka

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.