• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Samu Karbuwa A Afirka Ta Hanyar Samar Da Abubuwa Masu Amfani

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya-bayan nan ne jaridar “Business Day” ta Najeriya, da sauran kafofin watsa labaru na kasar, suka ba da rahoton cewa, kamfanonin harhada magunguna na kasar Sin da ta Najeriya na shirin yin hadin gwiwa, don gina wata masana’antar harhada magunguna da darajarta ta kai dalar Amurka miliyan 100 a jihar Legas.

 

Akwai wasu muhimman batutuwa game da wannan hadin gwiwa: Na farko, kamfanonin kasar Sin da ke halartar aikin sun kware wajen samar da magungunan cutar kanjamau, kuma manufar gina masana’antar harhada magunguna ita ce inganta dogaro da kai a Najeriya ta fuskar aikin kiwon lafiya, musamman ma a fannin samar da magungunan hana yaduwar cutar kanjamau.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Ke Lebanon 
  • Shugaba Tinubu Ya Sake Aika Tallafin Buhun Shinkafa 18,500 Kebbi

Abu na biyu kuma shi ne, an samar da shirin kafa wannan masana’anta ne bayan da kamfanonin harhada magunguna na kasar Amurka da na Turai, irin su GSK da Sanofi, suka janye daga Najeriya kwanan nan. Bisa la’akari da hauhawar farashin kayayyaki, da karancin wutar lantarki, da tabarbarewar yanayin zuba jari, da sauran matsalolin da Najeriya ta fuskanta a shekarun nan, kamfanonin harhada magunguna na yammacin duniya sun zabi janye jiki daga kasar, duk da cewa yin hakan ya kara ta’azzara matsalar karancin magunguna a Najeriya.

 

Labarai Masu Nasaba

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Daga wannan kwatance na “wani bangare ya fita waje, yayin da wani ya shiga ciki”, za mu iya fahimtar wani abu mai zurfi, wato dalilin da ya sa kasashen Afirka ke maraba da goyon bayan kasar Sin shi ne:

Na farko, kamfanonin kasar Sin sun dace da muhallin Afirka.

 

Lokacin da kamfanonin kasashen Yamma suka kasa jurewa kuma suka fice daya bayan daya, a nasu bangare kamfanonin kasar Sin na shigowa. Wannan ya nuna karfin kamfanonin kasar Sin, musamman ma a fannonin takaita kudin da ake kashewa, da kuma tinkarar hadari. Wannan ne ya sa sau da dama da kasashen Afirka ke matukar bukatar samun jari, Sinawa ne kadai ke iya ba su goyon baya.

 

Na biyu, Sinawa na da niyyar biyan bukatun jama’ar kasashen Afirka.

Alkaluma daga Majalisar Dinkin Duniya da hukumomin Najeriya sun nuna cewa, a yanzu haka akwai mutane miliyan 2 da suka kamu da cutar kanjamau a Najeriya, tare da samun sabbin masu kamuwa da cutar 1,400 a duk mako, sannan cutar ta sa yara miliyan 1.2 zama marayu. Saboda haka, yadda ake taimakawa Najeriya samun karfin samar da magungunan cutar kanjamau, wani mataki ne na adalci, dake samar da taimakon gaggawa ga al’ummar kasar, musamman ma marasa galihu. Yin hakan ya dace da tunanin gargajiya na Sinawa, na mai da adalci a gaban moriya.

 

Na uku, kasar Sin tana kokarin cika alkawuran da ta dauka.

A gun taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka da aka yi a birnin Beijing na Sin a watan da ya gabata, kasar Sin ta gabatar da “Ayyuka 10 na hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka don tabbatar da zamanantarwa”, ciki har da “Aikin hadin gwiwa a fannin lafiya”, wanda ya kunshi sa kaimi ga kamfanonin kasar Sin don su zuba jari ga harkar samar da magunguna a Afirka, da inganta bangaren kiwon lafiyar jama’a a kasashen Afirka, da dai sauransu. Babu shakka, wannan aiki na gina masana’antar harhada magunguna a Najeriya, mataki ne na aiwatar da manufofin da aka gabatar a taron kolin da ya gudana.

 

Idan aka kwatanta da dimbin ayyukan hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, wannan aiki na kafa masana’antar harhada magunguna ba wani aiki mai matukar muhimmanci ba ne. Amma duk da haka, an tabbatar da kimar kasar Sin a Afirka ta hanyar gudanar da ire-iren wadannan ayyuka. Suna iya zama wata masana’antar harhada magunguna, ko madatsar ruwa, da layin dogo, da tashar samar da wutar lantarki ta zafin rana, da dai sauransu. Wato abubuwa ne masu amfani da za su taimaki al’ummar kasashen Afirka wajen magance matsaloli, da kuma samar musu da fa’ida ta zahiri. Dalilin da ya sa kasar Sin ke daukar wadannan matakai, shi ne tunaninta na hadin gwiwa da kasashen Afirka ta hanyar nuna gaskiya, da neman samar da hakikanin sakamako, da tabbatar da zumunta da sahihanci. Wannan tunani ya sa ake samun dangantakar hadin gwiwa mai amfanin juna tsakanin Sin da Afirka, har ma ya sa zumuntar dake tsakaninsu karfafa a kai a kai. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaNDLEASin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Tinubu Ya Sake Aika Tallafin Buhun Shinkafa 18,500 Kebbi

Next Post

Wakilin Sin Ya Bukaci A Kyautata Tsarin Duniya Da Gyara Rashin Adalci Da Aka Yi Wa Afirka

Related

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

53 minutes ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

8 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

10 hours ago
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

20 hours ago
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci
Daga Birnin Sin

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

22 hours ago
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

23 hours ago
Next Post
Wakilin Sin Ya Bukaci A Kyautata Tsarin Duniya Da Gyara Rashin Adalci Da Aka Yi Wa Afirka

Wakilin Sin Ya Bukaci A Kyautata Tsarin Duniya Da Gyara Rashin Adalci Da Aka Yi Wa Afirka

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.