Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian ya bayyana cewa, domin kiyaye ka’idar kasar Sin daya tak a duniya da kuma karfin ikon kudurorin da suka dace na babban taron zauren Majalisar Dinkin Duniya da na Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), kasar Sin ta yanke shawarar kin amincewa Taiwan ta halarci babban taron WHO na bana.
Jami’in ya bayyana haka ne a wurin taron manema labaru na yau da kullum da aka yi a yau Alhamis 15 ga watan nan.
- Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
- Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci
An ba da rahoton cewa, za a bude babban taron kiwon lafiya na duniya karo na 78 a ranar 19 ga watan Mayu. Har zuwa yanzu dai, Taiwan ba ta sami goron gayyatar halartar taron ba.
Da yake ba da amsar wata tambayar da dan jarida ya yi masa, Lin Jian ya bayyana cewa, matsayin kasar Sin game da shigar Taiwan cikin ayyukan kungiyoyin kasa da kasa, ciki har da hukumar lafiya ta duniya, ya kasance a bayyane, wato dole ne a yi shi bisa ka’idar kasar Sin guda daya tak a duniya, wadda kuma ita ce muhimmiyar ka’ida da kudurin Majalisar Dinkin Duniya mai lamba 2758 da kuma kudurin taron kiwon lafiya na duniya mai lamba 25.1 suka tabbatar. Kana matukar ba a samu izinin gwamnatin tsakiya ba, Taiwan na kasar Sin, ba ta da wani dalili ko ’yancin shiga taron na WHO.
Lin Jian ya yi nuni da cewa, mahukuntan jam’iyyar DPP a Taiwan sun nuna taurin kai game da matsayinsu na ’yan aware a kan ’yancin kai na Taiwan, lamarin da ya kawar da hujjar siyasa ta halartar Taiwan taron kiwon lafiya na duniya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp