ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Gaggauta Tsagaita Bude Wuta A Sudan

by CMG Hausa
3 years ago
Sudan

Jiya Talata 25 ga watan nan ne kwamitin sulhu na MDD, ya yi tattaunawar gaggawa game da halin da ake ciki a kasar Sudan. Yayin zaman, wakilin kasar Sin ya yi kira ga bangarori 2, masu ruwa da tsaki a rikicin kasar ta Sudan, da su hanzarta tsagaita bude wuta a tsakaninsu, tare da bukatar kasashen duniya da su girmama ikon mulkin kan Sudan, da ba ta damar ba da jagoranci, da sauraren ra’ayoyin Sudan da kasashen da ke yankin ta.

A nasa bangare kuwa, babban magatakardan MDD António Guterres, ya sake jaddada cewa, tilas ne a gaggauta dasa aya ga wannan rikici. Ya kuma yi kira da a tsagaita bude wuta nan take, tare da bukatar kasashe mambobin kwamitin sulhu, da kasashen da ke yankin, su matsa wa bangarorin 2 na Sudan lamba, a kokarin sassauta zaman dardar a kasar.

  • Babu Wani Dan Nijeriya Da Ya Rasa Ransa A Rikicin Sudan – Gwamnatin Tarayya

Shi ma zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Zhang Jun, cewa ya yi a matsayinta na abokiya, kuma aminiyar Sudan, kasar Sin ta yi bakin ciki game da sake barkewar fada a Sudan. Tana kuma kira ga bangarori 2 na Sudan, da su mayar da muradun kasa, da na jama’a a gaban komai, su tsagaita bude wuta cikin sauri, a kokarin kaucewa tabarbarewar halin da ake ciki a kasar.

ADVERTISEMENT

Zhang Jun ya kuma jaddada cewa, kasar Sin na goyon bayan ikon mulkin kan Sudan, da ’yancin mulkin cikakkun yankunanta, kana tana fatan ganin kura ta kwanta a Sudan cikin hanzari, ta yadda kasar za ta sake samun zaman lafiya, da kwanciyar hankali, ta kuma koma kan hanyar da ta dace ta raya kanta.

Kafofin yada labaru na Sudan sun ruwaito cewa, a daren jiya Talata, ma’aikatar lafiyar Sudan ta ce, mutane 460 sun rasa rayukansu, yayin da wasu 4,063 suka jikkata, sakamakon dauki ba dadin da dakarun Sudan, da rundunar RSF suka gwabza a sassan jihohi kasar 11. (Tasallah Yuan)

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Ma’aikatar Tsaron Jama’a Ta Kasar Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadi Game Da Matakin Hukumar Shari’ar Kasar Amurka

Ma’aikatar Tsaron Jama’a Ta Kasar Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadi Game Da Matakin Hukumar Shari’ar Kasar Amurka

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.