• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Wadda Za Ta Samar Da Karin Damamaki Ga Duk Duniya Aminiya Ce Ta Kasashe Masu Tasowa Har Abada

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Wadda Za Ta Samar Da Karin Damamaki Ga Duk Duniya Aminiya Ce Ta Kasashe Masu Tasowa Har Abada
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon sabuwar shekara, aka nada Qin Gang, a matsayin ministan harkokin wajen kasar, ya kuma fara kai ziyarar aiki a kasashen Afirka. Ziyarar da ministocin wajen kasar Sin ke kaiwa Afirka a farkon kowa ce shekara, wata al’ada ce ta diflomasiyya ta kasar Sin a cikin shekaru 33 a jere, ba wai kawai tana nuna kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin Sin da Afirka ba, har ma tana nuna cikakken goyon bayan da kasar Sin ke bayarwa ga ci gaba da farfado da nahiyar Afirka, wadda ke da kasashe masu tasowa da dama.

A karshen shekarar 2022, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya je Riyadh, babban birnin kasar Saudiyya, don halartar taron koli na farko na Sin da kasashen Larabawa, da kuma taron kolin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Larabawa karo na farko, kana ya yi shawarwari da shugabannin kasashen Larabawa kusan 20, domin tsara hanyar gina al’ummar Sin da na Larabawa mai kyakkyawar makoma ta bai daya.

A watan Nuwamba na shekarar 2022, birnin Beijing ya tarbi shugaban kasar Latin Amurka da Caribbean na farko da ya kawo ziyara kasar Sin bayan babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 20, wanda shi ne sakataren farko na kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta Cuba, kuma shugaban kasar Miguel Díaz-Canel Bermúdez. A yayin ganawar, shugabannin kasashen biyu sun amince da yin hadin gwiwa tare don gina al’ummar Sin da Cuba mai makomar bai daya, a kokarin sa kaimi ga gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga bil’adama, tare da ciyar da dangantakar Sin da Latin Amurka a sabon zamani bisa daidaito,da samun moriyar juna, da kirkire-kirkire, da bude kofa, da kuma amfanar da jama’a gaba daya yadda ya kamata.

A yammacin ranar 16 ga watan Nuwamba na shekarar 2022, Xi Jinping ya tattauna da takwaransa na kasar Indonesia Joko Widodo a tsibirin Bali, inda suka cimma matsaya mai muhimmanci kan gina al’ummar Sin da Indonesia mai kyakkyawar makomar bai daya, sun kuma amince da yin amfani da bikin cika shekaru 10 da kafuwar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni tsakanin Sin da Indonesia a shekarar 2023, a matsayin wata dama ta samar da wani sabon salon hadin kai mai inganci.

Bugu da kari, bude kofa ga kasashen waje da yin hadin gwiwa su ne muhimman manufofin diplomasiyya da kasar Sin ta gudanar a sabon zamani. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi bayani sau da yawa ga duniya game da manufar Sin ta bude kofa ga kasashen waje, da ra’ayin Sin na sa kaimi ga raya tattalin arzikin duniya bisa tsarin bai daya, kana kasar Sin mai bude kofa za ta kara samar da dama ga duniya wajen samun ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

  • Hukumomin Cinikayyar Zimbabwe Za Su Shirya Taron Tattauna Bunkasa Huldar Kasuwanci Da Kasar Sin

 

A shekarar 2022, yawan kudin shige da ficen kayayyaki na kasar Sin ya zarce kudin Sin Yuan triliyan 40 a karo na farko, inda ta kiyaye matsayinta na kasa ta farko da ta fi yin cinikin kaya a duniya a shekaru 6 a jere. Wannan ya shaida cewa, Sin ta tsaya tsayin daka kan manufar bude kofa ga kasashen waje.

A ranar 18 ga watan Nuwanba na shekarar 2022, shugaba Xi Jinping ya bayyana a gun taron karba-karba na shugabannin kungiyar APEC cewa, a shekarar 2023, Sin za ta yi la’akari da gudanar taron dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar kasa da kasa na kasashe masu bin shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na 3, don samar da gudummawa wajen samun ci gaba da wadata a yankin Asiya da tekun Pasifik da duk duniya baki daya.

A gun bikin baje koli na kayayyakin da ake shigar da su kasar Sin karo na 5, shugaba Xi Jinping ya kara bayyana manufar Sin ta fadada bude kofa ga kasashen waje don samar da damar raya tattalin arzikin duniya ta bude kofa.

Bisa rahoton bude kofa na duniya na shekarar 2022 da aka gabatar, Sin ta samu nasarori wajen bude kofa ga kasashen waje, inda ta kasance kasa mai muhimmanci wajen sa kaimi ga bunkasa tattalin arzikin duniya, kana ta sauke nauyin dake wuyanta na gabatar da damarmakin kasuwanni ga duniya da kuma sa kaimi ga farfado da tattalin arzikin duniya. (Mai Fassara: Bilkisu Xin da Zainab Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lokaci Mafi Duhu A Sin Da Kafofin Watsa Labaru Na Kasashen Yammacin Duniya Suka Yi Hasashe, Ba Zai Tabbata Ba

Next Post

Dole A Hada Karfi Wajen Dakile Bazuwar Makamai A Afirka –Buhari

Related

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya
Daga Birnin Sin

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

16 hours ago
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

17 hours ago
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi
Daga Birnin Sin

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

20 hours ago
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

20 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

22 hours ago
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

22 hours ago
Next Post
Dole A Hada Karfi Wajen Dakile Bazuwar Makamai A Afirka –Buhari

Dole A Hada Karfi Wajen Dakile Bazuwar Makamai A Afirka –Buhari

LABARAI MASU NASABA

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

August 28, 2025
Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

August 28, 2025
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

August 28, 2025
Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

August 28, 2025
An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

August 28, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

August 28, 2025
Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

August 28, 2025
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

August 28, 2025
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

August 28, 2025
Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.