Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyana a jiya Talata cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasashen Afirka ciki har da Najeriya, da dimbin kasashe masu tasowa, wajen yin watsi da kariyar cinikayya, da yin adawa da danniya da cin zarafi, da bayyana karara muryar tabbatar da ra’ayin bangarori daban daban, da kare daidaici da adalci.
Wang ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Tuggar. Yana mai cewa, kasar Sin na maraba da Najeriya a matsayinta na abokiyar kawance don halartar taron BRICS, kuma tana goyon bayan Najeriya wajen taka rawa sosai a harkokin kasa da kasa da na shiyya-shiyya.
- Xi Jinping Ya Karfafawa Matasa Gwiwar Daukar Nauyin Daukaka Zamanantar Da Kasar Sin
- ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
A nasa bangaren, Tuggar ya ce, Najeriya za ta ci gaba da mutunta ka’idar Sin daya tak a duniya. Kana Najeriya ta yaba da matakin da kasar Sin ta dauka na soke haraji kan kayayyakin kasashen Afirka masu karamin karfi da ke da huldar diflomasiyya da ita, yana mai bayyana fatan kasar Sin za ta ci gaba da ba da taimako ga ci gaban yammacin Afirka.
Haka kuma Wang ya halarci taron ministocin waje na kasashe mambobin kungiyar BRICS da na kasashe kawayensu a wannan rana, inda aka tattauna game da yadda za a karfafa ra’ayin cudanyar bangarori daban daban.
Wang ya bayyana cewa, mafitar matsalolin da ake fuskanta a duniya ita ce kiyayewa da aiwatar da ra’ayin cudanyar bangarori daban daban. Ya ce bayan da ta habaka mambobinta, ya kamata kungiyar BRICS ta ci gaba yayata manufar yin shawarwari da juna da tabbatar da ci gaban juna da cin moriya tare, da kiyaye muhimman ka’idojin huldar kasa da kasa, da kuma kare tsarin ciniki tsakanin bangarori daban daban.
Wang ya jadadda cewa, amsar da Sin ta bayar game da yakin cinikayya a bayyane take, wato idan an dage kan yakin, ko kadan ba za mu ja da baya ba. Idan an shirya tattaunawa, dole ne mu girmama juna tare da yin zaman daidaito da juna. Ba don hakkinta na kanta ba ne, kasar Sin tana kuma kiyaye muradun bai daya na dukkanin kasashe. Abun da kasar Sin ke kiyayewa ba kawai hadin gwiwar cin moriyar juna ba ne, har ma da ka’idojin kasa da kasa. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp