• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashe Na Kara Maraba Da Sinawa Zuwa Kasashensu

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashe Na Kara Maraba Da Sinawa Zuwa Kasashensu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan da kasar Sin ta daidaita matakanta na yaki da annobar COVID-19, kasashe a fadin duniya ke murna da farin ciki, tare da maraba da miliyoyin Sinawa dake fatan kawo ziyarar yawon bude ido da ma kasuwanci a kasashensu.

Sassauta dokar takaita tafiye-tafiyen da ta fara aiki tun a ranar 8 ga watan Janairu, bayan tsawon shekaru 3 da barkewar annobar da ta addabi sassan duniya, na zuwa ne a daidai lokacin da al’ummar Sinawa a fadin duniya ke shirin bikin bazara ta sabuwar shekarar Zomo bisa kalandar gargajiya ta kasar Sin. Inda ake sa ran Sinawa za su yi biliyoyin tafiye-tafiye a cikin gida da ma kasashen waje, yayin bikin na kwanaki 7 da za a fara daga ranar 21 ga wata.

  • Amurka Ta Saba Amfani Da Annoba A Matsayin Makami

Saboda girman kasuwar kasar Sin, ya sa kasashe da yankuna na duniya, bayan samun wannan albishir, suka fara jan hankalin Sinawa, ta hanyar wallafa hotuna da bidiyon fitattun wuraren yawon shakatawa dake kasashensu a shafin Weibo.

Sai dai yayin da wasu kasashe ke murna da wannan mataki na kasar Sin, wasu kasashen yammacin duniya na neman siyasantar da matakan kamar yadda suka saba. Hali aka ce zanen dutse.

Masu fashin baki na cewa, matakin na kasar Sin zai ingiza farfadowar tattalin arzikin duniya, wanda ya fuskanci koma baya, sakamakon tasirin annobar COVOID-19. Wannan ne ma ya sa hukumar lafiya ta duniya (WHO) ta bukaci kasashen duniya, da su martaba matakai na kimiyya wajen yaki da wannan cuta, maimako nuna yatsa ga wata kasa da nufin mayar da hannun agogo baya, a kokarin da ake yi na ganin bayan wannan cuta.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Masu sharhi na cewa, abubuwan da suka faru a duniyar bil-Adama tsawon wadannan shekaru uku sanadiyar tasirin wannan annoba, ya ishi mai hankali darasi. Kukan kurciya dai jawabi ne, amma mai hankali ne kadai ke ganewa.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ta Fi Kawo Cikas Ga Aikin Yaki Da Cutar COVID-19 A Duniya

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Tare Da Yin Garkuwa Da Matan Aure 4 A Kaduna

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

16 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

17 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

18 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

19 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

21 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

2 days ago
Next Post
kudancin kaduna

'Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Tare Da Yin Garkuwa Da Matan Aure 4 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.