• English
  • Business News
Wednesday, July 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Duniya Na Kokarin Jan Hankalin Sinawa Matafiya Bayan Sake Bude Iyakokin Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashen Duniya Na Kokarin Jan Hankalin Sinawa Matafiya Bayan Sake Bude Iyakokin Kasar Sin

Chinese tourists arrive at Suvarnabhumi International Airport in Samut Prakarn province, Thailand, Monday, Jan. 9, 2023. Thailand is looking forward to hosting large numbers of vistors from China again after Beijing eased travel restrictions on Sunday. Chinese were about one-third of the total number of tourists visiting Thailand before the coronavirus pandemic, and the authorities hope they can help its lucrative tourism industry recover.(AP Photo/Sakchai Lalit)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashe a fadin duniya, musamman na yankin kudu maso gabashin Asiya, na murna dangane da tsammanin miliyoyin Sinawa masu tafiye-tafiye, bayan dage dokar takaita tafiye-tafiye a kasar.

A jiya Lahadi, 8 ga wata ne aka dage dokar takaita tafiye-tafiyen da aka ayyana shekaru 3 da suka gabata a kasar Sin biyo bayan barkewar annobar COVID-19. Sassauta dokar na zuwa ne a daidai lokacin da bikin bazara ta sabuwar shekarar gargajiya ta kasar Sin ke karatowa. Akwai yuwuwar Sinawa za su yi biliyoyin tafiye-tafiye a cikin gida da ma kasashen waje, yayin bikin na kwanaki 7 da za a fara daga ranar 21 ga wata.

  • Amurka Ba Ta Cancanci Zargin Wasu Sassan Ba Bayan Ta Gaza Shawo Kan COVID-19 A Cikin Gida

Sauyin matakan yaki da cutar dai ya samu matukar karbuwa daga kasashe da dama, ciki har da Thailand, da Malaysia, da Singapore, da Cambodia, da Indonesia, da Philippines, da New Zealand, kasashen dake matukar dokin karbar bakuncin Sinawa masu yawon shakatawa.

Hukumomin lura da fannin yawon bude ido a Thailand, sun ce kasar ta shirya tsaf domin karbar baki Sinawa, kuma suna fatan adadin Sinawa ’yan yawon shakatawa da kasar za ta karba a bana kadai, zai kai mutum a kalla miliyan 5, adadin da ya kai kusan rabin Sinawa miliyan 11.5 da suka ziyarci kasar a shekarar 2019.

Gwamnatoci a fadin duniya ba su tsaya bata lokaci ba wajen jan hankalin Sinawa matafiya saboda sassauta dokar a jiya, inda suka yi ta wallafa hotuna da bidiyon fitattun wuraren yawon shakatawa a shafin Weibo, wanda yake tamkar shafin Twitter a kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

Bayanai sun bayyana cewa, gangamin jan hankalin matafiya ya zo a kan gaba, bisa la’akari da karuwar bukatar tafiye-tafiye saboda zuwan bikin bazara. (Fa’iza Mustapha, Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Amurka Ta Raba Bayanan Annobar COVID-19 A Kan Lokaci

Next Post

Shugaba Buhari Ya Bude Wasu Manyan Aiyuka 6 A Jihar Yobe

Related

Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi

2 hours ago
Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

20 hours ago
Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu
Daga Birnin Sin

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

21 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

22 hours ago
Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

23 hours ago
Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi
Daga Birnin Sin

Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

1 day ago
Next Post
Shugaba Buhari Ya Bude Wasu Manyan Aiyuka 6 A Jihar Yobe

Shugaba Buhari Ya Bude Wasu Manyan Aiyuka 6 A Jihar Yobe

LABARAI MASU NASABA

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

July 23, 2025
An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

July 23, 2025
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

July 23, 2025
Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi

Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi

July 23, 2025
Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa

July 23, 2025
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati

July 23, 2025
Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

July 23, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Har Yanzu Yaƙi Da Ta’addanci Ne Babban Muradin Gwamnatina — Tinubu

July 23, 2025
Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa

Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa

July 23, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Katsina, Sun Jikkata Mutane 2, Sun Sace Wasu

July 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.