• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Duniya Suna Sa Ran Jin Muryoyin Kasar Sin A Taron Kolin G20

byCGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
G20

Ana gudanar da taron kolin shugabannin kungiyar G20 karo na 19 daga ranar 18 zuwa ranar 19 ga watan da muke ciki, a birnin Rio de Janeiro dake kasar Brazil. Jigon taron shi ne “gina duniya mai adalci da ci gaba mai dorewa”.

 

A cikin kwanakin nan, kasashen duniya sun bayyana fatansu na ganin Sin ta ba da sabbin damammaki na samar da ci gaba ga duniya a taron kolin G20 na wannan karo.

  • NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara
  • Kawu Sumaila Ya Yi Barazanar Maka Shugaban NNPP Na Kano A Kotu

Samun ci gaba, abu ne mai muhimmanci ga ko wace kasa. A karkashin hadin gwiwar kasashen G20, Sin ta dade tana mai da hankali kan batun ci gaba, ta fitar da kuma aiwatar da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya tare da shawarar bunkasa duniya da aka san ta da GDI, sannan tana maraba da kasashen mambobin G20 su shiga hadin gwiwa bisa shawarwarin, ta yadda za a tabbatar da ci gaban duniya tare.

 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

A cikin rukunin aiki na “yaki da yunwa da talauci” da kasar dake shugabancin taron kolin G20 na wannan karo wato kasar Brazil ta kafa, sau da dama ne Sin ta raba dabarunta na rage talauci da kirkire-kirkiren fasahohi, har ta kasance daya daga cikin kasashe mafi ba da gudunmawa. Ban da haka, abin da aka lura shi ne Sin ta dade tana jadadda samun ci gaba ta hanyar kirkire-kirkire, musamman ma a fannin tattalin arziki na zamani da samun ci gaba mara gurbata muhalli. A sa’i daya kuma, wata ajanda mai muhimmanci ta taron kolin G20 na wannan karo ita ce tattauna samun ci gaba ta fuskar rage fitar da iskar carbon mai dumama yanayi. Wannan ya sa kasashen duniya ke fatan ganin Sin za ta samar da babban kuzari wajen tabbatar da ci gaba mai dorewa a duniya.

 

A karkashin tsarin kungiyar G20, Sin ta sha yin kira da a aiwatar da ra’ayin kasancewar bangarori daban-daban, da kuma tsayawa tsayin-daka kan ra’ayin tattaunawa tare, da ginawa tare, da kuma rabawa tare wajen gudanar da harkokin duniya. Kasar Sin tana kuma sa kaimin tabbatar da karin gaskiya da adalci a wajen tafiyar da harkokin tattalin arzikin duniya, tare da kara fitowa da muryoyin kasashe masu tasowa.

 

Yayin taron kolin, Sin za ta tattauna batun samun ci gaba tare da bangarorin kasashe daban-daban, da kuma kira da karfafa kasancewar bangarori daban ddaban a duniya da kuma dunkulewar tattalin arzikin duniya. Saboda hakan, kasashen duniya suna fatan Sin za ta taimaka da basira da karfinta na samun ci gaba tare da inganta mulkin kasa da kasa ga kasashen duniya.(Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Ce Kasar Sin Da Birtaniya Na Da Dimbin Sararin Yin Hadin Gwiwa

Shugaba Xi Jinping Ya Ce Kasar Sin Da Birtaniya Na Da Dimbin Sararin Yin Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version