ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Sahel Na Bukatar Agaji Domin Yaki Ta’addanci -Rasha

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
Rasha

Rasha ta yi kira ga kasashen duniya su hada karfi da karfe wajen taimakon hadakar kasashen Alliance of Sahel States wato AES domin ba su taimakon da suke bukata a yakin da suke yi da matsalar tsaro.

Kasashen AES din su ne Mali da Burkina Faso da kuma Nijar wadanda suke karkashin mulkin soja bayan shugabannin mulkin kasashen sun hambarar da gwamnatin fararen hula.

  • Hadin Tuwon Dawa
  • Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

Kafar Actualite.bf mai zaman kanta ne ta ruwaito cewa Rasha ta gabatar da wannan kokon baran ne a jawabinta ga kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya, inda wakilinta na dindindin, Dmitry Chumakob ya ce kasashen na bukatar agajin tsaro.

ADVERTISEMENT

“Domin samun dawwamammen zaman lafiya, ya kamata kasashen duniya su ba kasashen Mali da Burkina Fasp da Nijar gudunmuwa,” in ji Chumakob.

Ya kara da cewa, “kasashen Afirka din ne da kansu suka fi sanin yadda za su magance matsalolin da suke fuskanta, kuma su ne suka fi sanin yadda za su yi yaki da matsalar tsaro da kuma hanyoyin inganta dimokuradiyya da tattalin arzikinsu.”

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Rasha dai ta zama babbar kawar kasashen na AES, wadanda ke jan jikinsu daga wasu kasashen na yamma, inda Moscow ta kuduri aniyar taimakon kasashen wajen yaki da masu tayar da kayar baya.

 

Nijer Ta Ceto ‘Yan Gudun Hijira Da Suka Makale A Libya

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun samu nasarar ceto ‘yancirani guda 50 da suke makala a sahara a hanyarsu ta tafiya kasar Libya.

RFI ta ruwaito cewa mutanen sun makale ne a kusa da bakin iyakar shiga kasar ta Libya bayan motarsu ta lalace a ranar 10 ga watan Agusta.

“Motarsu ta lalace ne a hanyarsu ta tafiya Libya, kasar da ake ratsawa domin tafiya kasashen turai. A ciki akwai fasinjoji 44 kuma motar tana tafiya ne a hanyar Madama-Dao da ke arewacin Nijar a lokacin da ta lalace, ta tsaya cak,” in ji rahoton na RFI.

Daga baya ne aka shiga neman motar, inda sojojin suka samu nasarar ceto su, sannan aka kai su garin Madama, inda ake cigaba da kula da su.

Sai dai har yanzu ba a tabbatar da asalin kasashen da mutanen suka fito ba, da kuma asalin kasar da suke shirin zuwa.

 

M23 Ta Musanta Zargin Kashe Gomman Fararen Hula A Kudancin Kibu

Kungiyar ‘yantawaye ta M23 a Congo ta musanta zarginta da ake yi da kashe gomman fararen hula a Kudancin Kibu na kasar, sannan kuma ta nanata cewa zarginta da ake yi da amfani da kananan yara a yaki kanzon kurege ne.

Kakakin M23, Willy Ngoma ne ya bayyana wa BBC haka, inda ya ce ko kadan ba ya cikin tsarinsu kai farmaki kan fararen hula.

“Ba ma kashe fararen hula. Ta yaya za mu kashe ‘yankasa, wadanda muke fafutikar karewa?

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
UNICEF Ya Jaddada Muhimmancin Yi Wa Yaran Afirka Rajistar Haihuwa

UNICEF Ya Jaddada Muhimmancin Yi Wa Yaran Afirka Rajistar Haihuwa

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.