• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kaska Za ta Mutu Da Haushin Kifi

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kaska Za ta Mutu Da Haushin Kifi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanin kowa ne cewa, kasar Sin daya ce tak a duniya, kuma yankin Taiwan wani yanki ne cikin kasar Sin wanda ba za a iya taba raba shi daga kasar Sin ba. Kuma, gwamnatin Jamhuriyyar Jama’ar Kasar Sin, ita ce halastacciyar gwamnati daya tilo dake wakiltar kasar Sin bisa doka. Wannan shi ne muhimmin bayani game da manufar “Kasar Sin daya tak a duniya”, wanda ya samu amincewar gamayyar kasa da kasa.

Duk da cewa kasar Amurka na daga cikin kasashen da suka amince da wannan manufa, baya ga sanarwoyi uku da kasashen biyu suka aminta da su a kan alakar dake tsakaninsu, amma a wasu lokuta ta kan yi biris tare da neman lalata tushen siyasa na huldar dake tsakaninta da kasar Sin, inda take ci gaba da hulda da yankin Taiwan na kasar Sin a hukumance, har da neman sanya ta cikin tsarin hukumomin MDD, kamar babban taron majalisar kiwon lafiya ta duniya.

  • Nuna Bambanci A Fannin Ba Da Ilmi Na Lahanta Makomar Amurka

Sanin kowa ne cewa, Taiwan ba kasa ba ce, wani bangare ne na kasar Sin. Duk wani kokari na neman jirkita gaskiya, ko kadan ba zai taba yin nasara ba, wato babban yanki da kuma yankin Taiwan duka suna karkashin ikon Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin ne.

Haramtaccen matakin Amurka na baya-bayan nan shi ne labarin da shafin intanet na Fadar White House na kasar Amurka ya walllafa cewa, gwamnatin Amurka za ta taimakawa yankin Taiwan na kasar Sin da makamai da horo a fannin soja wadda darajarta ta kai Amurka miliyan 345. Shi ne karo na farko da gwamnatin Biden ta samar da taimakon soja ga yankin Taiwan ta hanyar amfani da “ikon shugaba”.

Wannan mataki na Amurka ya saba yarjejeniyoyin kasa da kasa, kuma tsoma baki ne karara a harkokin cikin gidan kasar, wanda zai kawo illa matuka ga ikon mulki da tsaron kasar Sin, da ma kawo barazana mai tsanani ga zaman lafiya dake kasancewa tsakanin bangarori biyu na mashigin tekun Taiwan. Hali aka ce zaren Dutse.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Kamar yadda ruwa da wuta ba za su hadu wuri daya ba, haka ma burin ballewar yankin Taiwan, ya saba da burin wanzar da zaman lafiya da daidaito a zirin na Taiwan. Kuma domin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a zirin Taiwan, ya zama wajibi a tabbatar da rashin amincewa da duk wani mataki na ingiza burin “samun ’yancin kan Taiwan”. Burin Amurka da ’yan kanzaginta na neman tayar da husuma a yankin Taiwan, ba zai taba yin nasara ba. Haka kaska za ta mutu da haushin kifi. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwarzo, Bagudu Da Matawalle Na Cikin Jerin Ministocin Tinubu, Kashi Na Biyu

Next Post

Kungiyoyin Magoya Bayan Kano Pillars Da Katsina United Sunyi Taro A Kano Domin Sulhunta Tsakanin Su

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

16 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

17 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

19 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

19 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

21 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

23 hours ago
Next Post
Kungiyoyin Magoya Bayan Kano Pillars Da Katsina United Sunyi Taro A Kano Domin Sulhunta Tsakanin Su

Kungiyoyin Magoya Bayan Kano Pillars Da Katsina United Sunyi Taro A Kano Domin Sulhunta Tsakanin Su

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.