• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasuwanci Tsakanin Sin Da Zimbabwe Ya Bunkasa

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasuwanci Tsakanin Sin Da Zimbabwe Ya Bunkasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin jakadancin Sin dake kasar Zimbabwe ya bayyana cewa, cinikayya tsakanin Sin da Zimbabwe a cikin watanni 9 na farkon bana, ya karu da kashi 39.4 cikin 100, zuwa dalar Amurka biliyan 2.43, idan aka kwatanta da makamancin lokaci a shekarar da ta gabata, wanda ya zarce jimillar cinikin da aka yi a shekarar 2022.

A cewar ofishin jakadancin, darajar kayayyakin da Zimbabwe ta fitar zuwa kasar Sin a cikin wannan lokaci, ta kai dalar Amurka biliyan 1.36, yayin da darajar kayayyakin da aka shigo da su cikin kasar daga kasar Sin, ta kai dalar Amurka biliyan 1.07. Yana mai cewa, kayayyakin da kasar Sin ta ci gaba da shigo da su cikin kasar, sun taimakawa Zimbabwe wajen samun rarar cinikayyar da ta kai dalar Amurka miliyan 29.

  • Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka
  • Me Ya Sa Dangantaka Da Sin Ke Samun Karbuwa A Afrika?

A cewar hukumar kididdiga ta kasar Zimbabwe, a cikin watan Agusta, kasar Sin ta kasance kasa ta uku wajen fitar da kayayyaki zuwa kasar Zimbabwe, inda makwabciyarta Afrika ta Kudu ta kasance a kan gaba, sai hadaddiyar daular Larabawa a matsayin babbar kasuwa ta biyu a fannin fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje. Dangane da shigo da kayayyaki kuwa, a watan Agusta, kasar Sin ta kasance babbar kasuwa ta biyu ga Zimbabwe, bayan Afirka ta Kudu.

Sannan a yau Laraba 25 ga watan Oktoba, ranar yaki da kakaba takunkumi ce da kungiyar raya kudancin Afirka ko kuma SADC a takaice ta ayyana. Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning ta bayyana cewa, kasarta ta sake kira ga wasu kasashe da kungiyoyi ’yan kalilan, da su saurari muryoyin kasashe daban-daban, da gaggauta soke takunkuman da suka kakabawa kasar Zimbabwe ba bisa doka ba, da daukar matakai a zahirance, don taimaka mata habaka tattalin arziki da kyautata rayuwar al’umma, gami da taka rawar gani a fannin shimfida zaman lafiya da samar da ci gaba a duniya baki daya.

Mao ta jaddada cewa, Sin za ta ci gaba da goyawa Zimbabwe baya wajen nuna adawa ga shisshigin da wasu kasashe suka yi mata, don ta kama tafarkin samar da ci gaba bisa ’yancin kanta. (Ibrahim Yaya, Murtala Zhang)

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinZimbabwe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Tabbatar Da Zaben Tambuwal

Next Post

UNESCO Ta Yi Bikin Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yada Bayanai Ta Duniya A Abuja

Related

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

4 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

5 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

6 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

7 hours ago
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Daga Birnin Sin

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

8 hours ago
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

9 hours ago
Next Post
UNESCO Ta Yi Bikin Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yada Bayanai Ta Duniya A Abuja

UNESCO Ta Yi Bikin Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yada Bayanai Ta Duniya A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.