• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kauyukan Yawan Shakatawa Na Sin Na Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

byCGTN Hausa
2 years ago
Sin

Karin kauyukan kasar Sin masu bude kofa ga ’yan yawon bude ido na samun karbuwa, da jawo ra’ayin al’ummun kasashen duniya daban daban. A kwanan nan ma karin irin wadannan kauyuka 4, sun shiga jerin “Kauyuka Mafiya Kayatarwa” na duniya na shekarar 2023, bisa jadawalin hukumar lura da yawon bude ido ta MDD ko UNWTO.

Sabbin kauyukan da suka shiga jadawalin a wannan karo sun hada da Huangling na lardin Jiangxi, da Xiajiang na lardin Zhejiang, da Zhagana na lardin Gansu. Sai kuma Zhujiawan na lardin Shaanxi. Kafin su akwai kauyukan Yucun na lardin Zhejiang, da Xidi na lardin Anhui, wadanda tun a shekarar 2021 suka yi nasarar shiga jadawalin na hukumar UNWTO.

  • An Samu Karuwar Masu Rajistar Sabbin Sana’o’i A Kasar Sin
  • Kowa Ya Gyara Ya Sani

Har ila yau, akwai kauyen Dazhai na jihar Guangxi ta kabilar Zhuang mai cin gashin kanta, da Jingzhu dake karkashin birnin Chongqing, wadanda suka shiga jadawalin a shekarar 2022. Bisa hakan, kasar Sin mai irin wadannan kauyuka har guda 8, ta zamo ta daya a duniya a yawan “Kauyuka mafiya kayatarwa” na yawon shakatawa dake cikin jadawalin hukumar ta UNWTO.

Hakika yawon shakatawa muhimmin fanni ne na raya al’adu, da musayar su, da sada zumunta tsakanin al’ummun sassan duniya daban daban, kana wata dama ce ta nishadantarwa, da samar da kudaden shiga, da guraben ayyukan yi, wanda hakan ke raya tattalin arzikin duniya baki daya.

A fannin yawon shakatawa mai alaka da kauyuka kuwa, ma iya cewa hakan wata dama ce ta bunkasa ci gaban yankunan karkara dake sassa daban daban na duniya, kana hakan na baiwa al’ummun duniya damar kiyaye al’adun gargajiya da ake gada daga kaka da kakanni, ciki har da na kayayyaki, da wadanda ba na kayayyaki ba, da fannin noma, da kare kyakkyawan yanayin muhallin halittu da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Ko shakka babu kasar Sin ta yi rawar gani a fannin inganta wannan sashe, musamman a shekarun baya bayan nan, inda har ma ma’aikatar raya al’adun kasa da yawon bude ido ta kasar, ta ce an kai ga kyautata kauyukan yawon bude ido a matakin kasa har guda 1,597, wanda hakan ya ingiza harkar bude ido a sassa daban daban na karkarar kasar.

Yayin da duniya ke mayar da hankali ga raya karin sassan tattalin arziki, da kyautata muhalli da muhallin halittu, fadada fannin yawon bude ido na kauyuka da Sin ke yi abun a yaba ne, kuma abun koyi ga kasashe masu tasowa da dama dake da irin wannan fifiko.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
Duniya

Tsaron Da Muke Fatan Gani A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version