ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kowa Ya Gyara Ya Sani

by CGTN Hausa
3 years ago
Sani

Kasar Sin ta bayyana kudurinta na ci gaba da yin hadin gwiwa tare da dukkan bangarori, da kuma ba da himma da daukar matakai masu ma’ana a kwamitin sulhu na MDD, domin kawo karshen tashin hankali a zirin Gaza, da aiwatar da hanyoyin warware shirin kafa kasashe biyu, da samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin gabas ta tsakiya. 

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ce ta bayyana hake, a lokacin da take karin haske kan kuduri mai lamba 2720 da kwamitin sulhu na MDD ya amince da shi game da rikicin Palasdawa da Isra’ila, inda ta yi kira da a dauki matakin gaggawa na fadada ayyukan jin kai a zirin Gaza da samar da yanayi mai dorewa da kawo karshen tashin hankali.

  • Sin: An Fitar Da Shirin Gaggauta Gina Ingantaccen Tsarin Ayyukan Lissafin Na’urori Masu Kwakwalwa Mai Karfi Na Kasa
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Gudanar Da Taron Tunawa Da Cika Shekaru 130 Da Haihuwar Mao Zedong

Idan ba a manta ba, kasar Sin ta kada kuri’ar amincewa da kuduri mai lamba 2720, wanda shi ne kuduri na biyu da kwamitin sulhun ya amince da shi tun barkewar rikicin Falasdinu da Isra’ila. Ta kuma bayyana cewa, kudurin bai zo daidai da yadda kasashen duniya suke tsammani ba kuma yana da wasu gibi da ya kamata a cike su.

ADVERTISEMENT

A yayin da ya zuwa yanzu rikicin Falasdinu da Isra’ila ya yi sanadiyar mutuwa da raunata dubban fararen hula, kana kuma yanayin jin kai a Gaza ke ci gaba da tabarbarewa, Sin ta bukaci da a aiwatar da kudurin yadda ya kamata, da fadada taimakon jin kai, da samar da hanyar sanya ido nan da nan. A cewar masu fashin baki, matakin na kasar Sin bai zo da mamaki ba, duba da irin matakai da shawarwarin da take bayarwa a duk lokacin da bukatar hakan ta taso, wajen ganin an kawo karshen duk wani tashin hankali dake faruwa a sassan duniya. Har kullum kasar Sin na matukar adawa, tare da yin tir da dukkanin wasu hare-haren da ake kaiwa fararen hula.

Sanin kowa ne cewa, tsagaita bude wuta shi ne abu mai muhimmanci da ake bukata. Kuma kasar Sin ta jaddada kudurinta na yin hadin gwiwa da dukkan bangarori masu kaunar zaman lafiya wajen inganta hadin gwiwa, da daukar managartan matakai don kawo karshen tashe-tashen hankula a zirin Gaza, da aiwatar da shawarwarin kafa kasashen biyu, da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin gabas ta tsakiya. Wannan ya kara tabbatar da aniya da burin kasar Sin mai kaunar zaman lafiya, na gina duniya mai kwanciyar hankali da kowa zai ji dadin zama a cikinta. Sabanin yadda wasu kasashe ke kara rura wutar tashin hankali, ta hanyar nuna goyon baya ga wani bangare, domin cimma muradunsu na kashin kai, ba kuma tare da la’akari da yadda sakamakon hakan zai haifar ga fararen hula da ma kokarin da ake ba dare ba rana na neman wanzar da zaman lafiya a duniya ba. Amma kowa ya yi na gari don kansu. (Ibrahim Yaya)

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Sani
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Hadin Kan Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Zuba Jari Game Da Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ya Samu Ci Gaba Akai-Akai A Bana

Hadin Kan Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Zuba Jari Game Da Shawarar "Ziri Daya Da Hanya Daya" Ya Samu Ci Gaba Akai-Akai A Bana

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.