ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kowa Ya Gyara Ya Sani

by CGTN Hausa
3 years ago
Sani

Kasar Sin ta bayyana kudurinta na ci gaba da yin hadin gwiwa tare da dukkan bangarori, da kuma ba da himma da daukar matakai masu ma’ana a kwamitin sulhu na MDD, domin kawo karshen tashin hankali a zirin Gaza, da aiwatar da hanyoyin warware shirin kafa kasashe biyu, da samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin gabas ta tsakiya. 

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ce ta bayyana hake, a lokacin da take karin haske kan kuduri mai lamba 2720 da kwamitin sulhu na MDD ya amince da shi game da rikicin Palasdawa da Isra’ila, inda ta yi kira da a dauki matakin gaggawa na fadada ayyukan jin kai a zirin Gaza da samar da yanayi mai dorewa da kawo karshen tashin hankali.

  • Sin: An Fitar Da Shirin Gaggauta Gina Ingantaccen Tsarin Ayyukan Lissafin Na’urori Masu Kwakwalwa Mai Karfi Na Kasa
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Gudanar Da Taron Tunawa Da Cika Shekaru 130 Da Haihuwar Mao Zedong

Idan ba a manta ba, kasar Sin ta kada kuri’ar amincewa da kuduri mai lamba 2720, wanda shi ne kuduri na biyu da kwamitin sulhun ya amince da shi tun barkewar rikicin Falasdinu da Isra’ila. Ta kuma bayyana cewa, kudurin bai zo daidai da yadda kasashen duniya suke tsammani ba kuma yana da wasu gibi da ya kamata a cike su.

ADVERTISEMENT

A yayin da ya zuwa yanzu rikicin Falasdinu da Isra’ila ya yi sanadiyar mutuwa da raunata dubban fararen hula, kana kuma yanayin jin kai a Gaza ke ci gaba da tabarbarewa, Sin ta bukaci da a aiwatar da kudurin yadda ya kamata, da fadada taimakon jin kai, da samar da hanyar sanya ido nan da nan. A cewar masu fashin baki, matakin na kasar Sin bai zo da mamaki ba, duba da irin matakai da shawarwarin da take bayarwa a duk lokacin da bukatar hakan ta taso, wajen ganin an kawo karshen duk wani tashin hankali dake faruwa a sassan duniya. Har kullum kasar Sin na matukar adawa, tare da yin tir da dukkanin wasu hare-haren da ake kaiwa fararen hula.

Sanin kowa ne cewa, tsagaita bude wuta shi ne abu mai muhimmanci da ake bukata. Kuma kasar Sin ta jaddada kudurinta na yin hadin gwiwa da dukkan bangarori masu kaunar zaman lafiya wajen inganta hadin gwiwa, da daukar managartan matakai don kawo karshen tashe-tashen hankula a zirin Gaza, da aiwatar da shawarwarin kafa kasashen biyu, da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin gabas ta tsakiya. Wannan ya kara tabbatar da aniya da burin kasar Sin mai kaunar zaman lafiya, na gina duniya mai kwanciyar hankali da kowa zai ji dadin zama a cikinta. Sabanin yadda wasu kasashe ke kara rura wutar tashin hankali, ta hanyar nuna goyon baya ga wani bangare, domin cimma muradunsu na kashin kai, ba kuma tare da la’akari da yadda sakamakon hakan zai haifar ga fararen hula da ma kokarin da ake ba dare ba rana na neman wanzar da zaman lafiya a duniya ba. Amma kowa ya yi na gari don kansu. (Ibrahim Yaya)

LABARAI MASU NASABA

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

Sani
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

MASU ALAKA

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin
Daga Birnin Sin

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

July 9, 2026
Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni
Daga Birnin Sin

Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

July 9, 2026
Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum
Daga Birnin Sin

Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

July 9, 2026
Next Post
Hadin Kan Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Zuba Jari Game Da Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ya Samu Ci Gaba Akai-Akai A Bana

Hadin Kan Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Zuba Jari Game Da Shawarar "Ziri Daya Da Hanya Daya" Ya Samu Ci Gaba Akai-Akai A Bana

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

July 10, 2026
Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

July 10, 2026
Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

July 10, 2026
Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.