• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kin Amincewa Da Kudurin Tsagaita Bude Wuta A Gaza Da Amurka Ta Yi Ya Kara Nuna Rashin Mutunci Da Adalcinta

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Kin Amincewa Da Kudurin Tsagaita Bude Wuta A Gaza Da Amurka Ta Yi Ya Kara Nuna Rashin Mutunci Da Adalcinta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 20 ga watan da muke ciki, kwamitin sulhu na MDD ya kada kuri’a kan daftarin kudurin tsagaita bude wuta a Gaza da mambobi 10 na kwamitin wadanda ba na dindindin ba suka gabatar. Kudurin ya samu kuri’u 14 na nuna amincewa, da kin yarda 1 daga Amurka.

 

Wannan ya kasance karo na 5 da Amurka take kin yarda da daftarin kudirin tsagaita bude wuta a Gaza tun barkewar rikicin zirin Gaza na wannan karon. Lokacin da Amurka ta nuna kin yarda da shi a karon farko a ranar 18 ga watan Oktoban na bara, jama’a fiye da 3000 sun rasa rayukansu a yankin, a halin yanzu wannan adadi ya karu zuwa 44000, amma Amurka ta ci gaba da hawan kujerar na ki a bangarenta.

  • Kamata Ya Yi Sin Da Amurka Su Mai Da Hankalinsu A Kan Ci Gaban Duniya
  • Za Mu Kawo Karshen Hukunce-Hukuncen Kotuna Masu Karo Da Juna – Minista

Rayukan mutum 44000 ba adadi ne kawai ba, ainihin rayuka ne. Jama’ar Gaza na mutuwa a cikin hare-haren da ake kai musu. Kasashen duniya na yin iyakacin kokarin fitar da hanyar da ta dace wajen warware wannan matsala, don hana tsananta halin da ake ciki a yankin. Amma, Amurka ta yi amfani da ikonta na kin amincewa sau da dama, har ma ta samarwa Isra’ila da tallafin makamai sau da dama, matakin da ya rika tsananta halin da ake ciki. A gaskiya abin kunya ne ga gwamnatin Amurka, wadda ta rasa jin tausayi ko nuna halin mutunci da adalci.

 

Labarai Masu Nasaba

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

Matakan soja da Isra’ila ta dauka a Gaza sun wuce matakin ceto mutanen da aka yi garkuwa da su, kuma gindaya sharadi wajen tsagaita bude wuta, tamkar rura wutar yaki ne da kisan jama’a. Daina bude wuta ba tare da sharadi ba nan da nan da tabbatar da shirin “samar da kasashe biyu” ita ce hanya daya tilo da za a warware wannan matsala. Don haka, bai kamata Amurka ta yi amfani da ikonta na hawan kujerar na ki a kwamitin sulhu ba don kare moriyarta da ba da kariya ga kawayenta. Amurka, dole ne ta nuna mutunci da kuma adalcinta a fili a kan wannan lamarin. (Mai zane da rubutu: MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dole Ne Ƙungiyoyin Ƴan Banga Su Haɗa Kai – Kauran Yauri

Next Post

Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Fiye Da Biliyan 465 A Matsayin Kasafin Kuɗin 2025

Related

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

3 days ago
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

4 days ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

1 week ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

2 weeks ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

2 weeks ago
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

3 weeks ago
Next Post
Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Fiye Da Biliyan 465 A Matsayin Kasafin Kuɗin 2025

Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Fiye Da Biliyan 465 A Matsayin Kasafin Kuɗin 2025

LABARAI MASU NASABA

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

August 11, 2025
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

August 11, 2025
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

August 11, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

August 11, 2025
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

August 11, 2025
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

August 11, 2025
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.