• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kin Amincewa Da Kudurin Tsagaita Bude Wuta A Gaza Da Amurka Ta Yi Ya Kara Nuna Rashin Mutunci Da Adalcinta

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Kin Amincewa Da Kudurin Tsagaita Bude Wuta A Gaza Da Amurka Ta Yi Ya Kara Nuna Rashin Mutunci Da Adalcinta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 20 ga watan da muke ciki, kwamitin sulhu na MDD ya kada kuri’a kan daftarin kudurin tsagaita bude wuta a Gaza da mambobi 10 na kwamitin wadanda ba na dindindin ba suka gabatar. Kudurin ya samu kuri’u 14 na nuna amincewa, da kin yarda 1 daga Amurka.

 

Wannan ya kasance karo na 5 da Amurka take kin yarda da daftarin kudirin tsagaita bude wuta a Gaza tun barkewar rikicin zirin Gaza na wannan karon. Lokacin da Amurka ta nuna kin yarda da shi a karon farko a ranar 18 ga watan Oktoban na bara, jama’a fiye da 3000 sun rasa rayukansu a yankin, a halin yanzu wannan adadi ya karu zuwa 44000, amma Amurka ta ci gaba da hawan kujerar na ki a bangarenta.

  • Kamata Ya Yi Sin Da Amurka Su Mai Da Hankalinsu A Kan Ci Gaban Duniya
  • Za Mu Kawo Karshen Hukunce-Hukuncen Kotuna Masu Karo Da Juna – Minista

Rayukan mutum 44000 ba adadi ne kawai ba, ainihin rayuka ne. Jama’ar Gaza na mutuwa a cikin hare-haren da ake kai musu. Kasashen duniya na yin iyakacin kokarin fitar da hanyar da ta dace wajen warware wannan matsala, don hana tsananta halin da ake ciki a yankin. Amma, Amurka ta yi amfani da ikonta na kin amincewa sau da dama, har ma ta samarwa Isra’ila da tallafin makamai sau da dama, matakin da ya rika tsananta halin da ake ciki. A gaskiya abin kunya ne ga gwamnatin Amurka, wadda ta rasa jin tausayi ko nuna halin mutunci da adalci.

 

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Matakan soja da Isra’ila ta dauka a Gaza sun wuce matakin ceto mutanen da aka yi garkuwa da su, kuma gindaya sharadi wajen tsagaita bude wuta, tamkar rura wutar yaki ne da kisan jama’a. Daina bude wuta ba tare da sharadi ba nan da nan da tabbatar da shirin “samar da kasashe biyu” ita ce hanya daya tilo da za a warware wannan matsala. Don haka, bai kamata Amurka ta yi amfani da ikonta na hawan kujerar na ki a kwamitin sulhu ba don kare moriyarta da ba da kariya ga kawayenta. Amurka, dole ne ta nuna mutunci da kuma adalcinta a fili a kan wannan lamarin. (Mai zane da rubutu: MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dole Ne Ƙungiyoyin Ƴan Banga Su Haɗa Kai – Kauran Yauri

Next Post

Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Fiye Da Biliyan 465 A Matsayin Kasafin Kuɗin 2025

Related

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

2 days ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

2 days ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

3 days ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

4 days ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

5 days ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

5 days ago
Next Post
Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Fiye Da Biliyan 465 A Matsayin Kasafin Kuɗin 2025

Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Fiye Da Biliyan 465 A Matsayin Kasafin Kuɗin 2025

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

September 7, 2025
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

September 7, 2025
Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

September 7, 2025
Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

September 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

September 7, 2025
Arewa

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

September 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

September 7, 2025
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

September 7, 2025
ASUU

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

September 7, 2025
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.