• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kingibe Ya Yaba Wa Tsare-tsaren Bunkasa Ilimi Ga Matasa Na Buratai

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
in Labarai
0
Kingibe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dattijo kuma tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Ambasada Babagana Kingibe, ya yaba wa Ambasada Tukur Yusufu Buratai bisa irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban ilimi a Nijeriya, musamman a fannin bunkasa jagoranci matasa da tunani mai zurfi.

Ambasada Kingibe, wanda ya yi wannan yabo a lokacin da yake jagorantar bikin bayar da lambar yabo ta 2024 na Adabin Matasa da kungiyar TY Buratai Literary Initiatibe (TYBLI) ta shirya, ya yaba da kwazon Buratai a kakarinsa na renon matasa.

  • Kamfanoni 80 Sun Bayyana Burinsu Na Halartar Baje Kolin CIIE Karo Na 8
  • Zargin Cin Zarafin Likita: Gwamna Yusuf Ya Roki Likitoci Su Bayar Da Kofar Sulhu

Da yake tunawa da shekarun da ya yi a aikin soja, Ambasada Kingibe ya tunatar da gagarumin sauyi da sojoji suka samu a lokacin jagorancinsa a matsayin shugaban soji da kuma kwazo da ci gaban tunani na hafsoshi da sojoji.

Ambasada Kingibe ya jaddada karfin adabi mai dorewa a matsayin ginshikin sadarwa mai inganci, duk da ci gaban ada aka samu ta fuskar ilimn fasahar zamani.

“Fasaha ba zai iya sauya salon rubutacciyar kalmar ba,” in ji shi, ya yi alkawarin hadin gwiwa a cikin shiri na gaba na TYBLI don ci gaba da horar da matasa masu basira a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

A nasa jawabin, babban mai masaukin baki kuma tsohon Hafsan Sojin Kasa, sannan tsohon jakadan Nijeriya a Jamhuriyar Benin, Laftanar Janar Tukur Yusufu Buratai mai ritaya, ya jaddada mahimmancin rubutu wajen ci gaban mutum, sadarwa, da jagoranci.

“Rubutu na da matukar muhimmanci wajen bunkasa ilimin mutum, hangen nesa, da kuma ikon sadarwa,” in ji shi. “Dole ne shugabanni su bayyana ra’ayoyinsu, kuma don ku bayyana kanku da kyau, dole ne ku rubuta.”

Da yake waiwaye kan kwarewarsa a matsayinsa na dan kungiyoyin adabi da wasan kwaikwayo a shekarunsa na makaranta, Buratai ya jaddada mahimmancin rubutu don ci gaban kansa, sadarwa, da jagoranci. “Dole ne shugabanni su bayyana ra’ayoyinsu.

Idan ba ku rubuta abin da kuke tunani ba, kuna iya mantawa da shi.

Amma da zarar ka rubuta shi, yana bude damar da za a amfana da al’umma.” A cewarsa.

Ya nuna godiya ga mahalarta taron, magoya baya, da abokan hadin gwiwa, ciki har da Hajiya Hauwa Aliyu da British Council.

Buratai ya kuma yi tsokaci kan shirin kara kudaden kyaututtuka da kuma yiwuwar bayar da tallafin karatu ga wadanda suka yi nasara a karatun sakandare ko na gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BurataiTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Kano Ya Gabatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Na Naira Biliyan 549.1

Next Post

‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

57 minutes ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

1 hour ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

2 hours ago
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
Labarai

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

3 hours ago
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
Labarai

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

4 hours ago
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule
Labarai

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

5 hours ago
Next Post
‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO

‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa - Hukumar FAO

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.