• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO

by Sulaiman and Abubakar Abba
8 months ago
in Noma Da Kiwo
0
‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar samar da abinci da kula da aikin noma ta duniya (FAO), ta sanar da cewa; a halin yanzu ‘yan Nijeriya miliyan 1.8 ne ke fama da matsalar yunwa.

Karamin Ministan Ma’aikatar Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Aliyu Sabi Abdullahi; ya sanar da hakan ne a Abuja, wajen taron manema labarai.

  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci
  • Kamfanoni 80 Sun Bayyana Burinsu Na Halartar Baje Kolin CIIE Karo Na 8

Sai dai, Abdullahi ya shelanta cewa; gwamnatin tarayya ta mayar da hankali wajen yakar rashin abinci a kasar, inda ya yi nuni da cewa; a 2023, mutane miliyan 733 ne ke fuskantar yunwa a dukkanin fadin duniya.

Ministan, wanda ya bayyana haka a bikin ranar abinci ta duniya da aka gudanar a kwanakin baya ya ci gaba da cewa, bisa rahoton yanzu da hukumar FAO ta wallafa kan karancin abinci da kuma abinci mara gina jiki da mutane ke fuskanta ya kai miliyan 733 a 2023 a fadin duniya.

Ya kara da cewa, kimanin mutane biliyan 2.33 sun fuskanci karancin abinci a 2023, inda kuma mutane biliyan 2.8 a 2022, ba sa iya samun abinci mai gina jiki.

Labarai Masu Nasaba

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Ya yi gargadin cewa, idan har mahukunta a kasar ba su dauki matakan da suka kamata ba, kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 582 ne za su fuskanci rashin samun abinci mai gina jiki nan da 2030.

Abdullahi ya sanar da cewa, akwai manyan kalubale da dama da suka haifar da karancin abinci a duniya da suka hada da sauyin yanayi, fari, yawan samun ruwan sama da sauransu.

A cewar tasa, wadannan kalubalen sun kasance barazana a kan harkokin noma baki-daya, sannan kuma ya danganta da karancin abincin da ake ci gaba da samu a kasar sakamakon rashin tsaro, matsin tattalin arziki, annobar ambaliyar ruwan sama da kuma cire tallafin mai.

Sai dai, ya sanar da cewa; don mangance wadannan kalubale, wadanda kuma suka zamo karfen kafa wajen cimma burin da gwamnatin tarayya ta sanya a gaba na samar da wadataccen abinci a kasar, gwamnatin ta wanzar da sauye-sauye da dama da suka hada da kirkiro da ayyukan yi da kuma rage tsadar kayan abinci.

Ya kara da cewa, dole ne har sai masu ruwa da tsaki a wannan kasa, su ma sun bayar da tasu gudunmawar; kafin a iya kawo karshen wadannan matsaloli.

A cewarsa, a shekarar 2017; Nijeriya ta samu gagarumar nasara a fannin aikin noma a duniya, inda ta kai mataki na daya a fannin noman Rogo da Doya, inda ta noma wadannan amfani da suka kai kimanin tan miliyan 59.4 da kuma tan miliyan 47.9 baki-daya.

Bugu da kari, ya kara da cewa; Nijeriya ta kai mataki na 14 wajen noman Masara, inda ta noma tan miliyan 10.42; ta kai mataki na hudu a fannin noman Kwakwar manja, inda ta noma tan miliyan 7.7 a cikin shekara guda.
Kazalika a 2019, Nijeriya ce kan gaba wajen noman Shinkafa a dukkanin Nahiyar Afirka, inda aka noma tan miliyan tara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kangin TalauciYunwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kingibe Ya Yaba Wa Tsare-tsaren Bunkasa Ilimi Ga Matasa Na Buratai

Next Post

Gwamnatin Tarayya Da EU Sun Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Wutar Lantarki

Related

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

2 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

1 week ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

1 week ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

2 weeks ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Next Post
Discos

Gwamnatin Tarayya Da EU Sun Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.