• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiyaye Rayukan Al’umma: Majalisa Na Shirin Keɓe Wa Masu Sayar Da Iskar Gas Wuri A Wajen Birnin Kano

by Sulaiman
11 months ago
Iskar gas

Majalisar dokokin jihar Kano ta fara yunkurin garambawul ga dokar hukumar kashe gobara ta jihar mai lamba 17 ta shekarar 1970 domin sanya wani sashe na doka kan yawaitar masu sayar da iskar gas – na girki a cikin birnin Kano.

 

Hakan ya biyo bayan gabatar da rahoton da kwamitin kula da ayyuka na musamman ya gabatar a kan binciken da ya yi kan sayar da iskar gas a cikin unguwanni a yayin zaman majalisar da kakakin majalisar Hon. Ismail Falgore ya jagoranta.

  • Majalisar Dokokin Kano Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Gyaran Dokar Haraji A Nijeriya
  • An Gudanar Da Dandalin Tattaunawa Tsakanin Kafofin Watsa Labarai Na Bidiyo Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Birnin Quanzhou

Da yake gabatar da rahoton, shugaban kwamitin wanda kuma shi ne mamba mai wakiltar mazaɓar Gezawa, Abdullahi Yahaya, ya bayyana cewa, hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta bayar da rahoton kimanin gidaje 475 na masu sayar da iskar gas ba bisa ka’ida ba bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki a jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

Ya kuma kara da cewa, alkaluman da hukumar sa ido kan harkokin man fetur ta Nijeriya (NMDPRA) reshen jihar Kano ta fitar ya nuna cewa, akwai masu sayar da iskar gas guda 234 da ba su da lasisi a jihar.

 

A cewarsa, an gudanar da binciken ne biyo bayan wani kudiri da dan majalisa mai wakiltar mazaɓar Kiru, Hon. Tasiu Abubakar ya gabatar game da hatsarin da ke tattare da sayar da iskar gas acikin al’umma da kuma buƙatar samar masu wasu keɓaɓɓun wurare domin kiyaye rayuka da dukiyoyin al’umma.

 

Shugaban kwamitin ya ce, binciken ya takaita ne a kan babban birnin Kano, kuma ‘yan kadan ne daga cikin masu sayar da iskar gas din da suka yi rajista da NMDPRA.

 

Sai dai kwamitin ya ba da shawarar cewa, ya kamata gwamnatin jihar ta samar da wurin dindindin ga masu sayar da iskar gas a kofofin shiga birnin Kano guda shida, kamar dai yadda ta yi wa masu sayar da magunguna da wayar salula a jihar, inda ta kebe musu wuri daban.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

sallah
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
Next Post
Hukumar NDLEA Ta Kama Mutane 14,480 A Cikin Watanni 10 – Marwa

Hukumar NDLEA Ta Kama Mutane 14,480 A Cikin Watanni 10 – Marwa

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

October 15, 2025
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

October 15, 2025
Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.