• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Ba Na Cikin Gwamnati Ba Zan Shiga Zanga-zanga Ba – Abdulaziz Abdulaziz

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Ko Ba Na Cikin Gwamnati Ba Zan Shiga Zanga-zanga Ba – Abdulaziz Abdulaziz
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai taimaka wa shugaban ƙasa a kan kafafen yada labarai, Abdulaziz Abdulaziz, ya bayyana cewa ko baya cikin gwamnatin Bola Tinubu, ba zai shiga zanga-zangar da ake kokarin yi a watan Agusta ba. 

Abdulaziz, ya bayyana haka ne a shafinsa Facebook a safiyar yau Laraba, inda ya mayarwa da waɗanda suke nemo tsofaffin rubuce-rubucensa na baya da ya yi na shiga zanga-zanga.

  • Babu Tabbacin Ko Ederson Zai Ci Gaba Da Zama A Manchester City – Guadiola
  • Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin ‘Yan Matan Chibok

Ya ce “Masu tone-tonen tsoffin rubutuna ba sai kun ba wa kanku wahala ba!

“Na shiga zanga-zanga guda biyu a baya. Na shiga ta cire tallafin man fetur a 2012 a Kano na kuma shiga ta ‘Bring Back Our Girls’ a Abuja a 2014. Duka wadancan zanga-zanga suna da tsari da shugabanci da kuma sanin inda aka dosa.

Yawanci kafin fita zanga-zanga ana fitar da tsarin yadda za ta gudana da kuma irin abin da masu zanga-zangar suke buƙata, hakan ya sa Abdulaziz ya ce wannan ba ta da tsarin da ya kamata a shiga.

Labarai Masu Nasaba

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

“Amma a 2019 ban shiga zanga-zangar ENDSARS ba saboda (kamar yadda na faɗa a wancan lokacin) ba ta da tsarin shugabanci da takamammiyar manufa (idan ban da ƙoƙarin tunzura mutane da yi wa gwamnati tawaye wadda kuma kan kai ga jefa ƙasa cikin ruɗani). Na ɗauki wannan matsayar ne duk da bani da alaƙa ta kusa ko ta nesa da gwamnatin Buhari.

“Zanga-zangar da ake shirin yi ta August b ata da bambanci da ta Endsars don haka ko da ba na cikin gwamnati ba zan taɓa goyon bayanta ba.”

Batun zanga-zanga dai shi ne abin da ake yawan tattaunawa a shafukan sada zumunta a Nijeriya a ‘yan kwanakin nan, sai dai har yanzu ba a san jagororin zanga-zangar ba.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta bakin ministan yaɗa labarai, ya roƙi matasan da suke shirya zanga-zangar da cewa su sake bashi lokaci domin ya saisaita lamuran ƙasar nan.

Sai dai tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, wanda kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa ne a jam’iyyar adawa ta PDP, ya soki gwamnatin tarayya, inda ya ce waɗanda suke cewa ka da a yi zanga-zangar su ne waɗanda suka jagoranci wadda aka yi a baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abdulaziz AbdulazizSiyasaTinubuTsadar RayuwaZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Babu Tabbacin Ko Ederson Zai Ci Gaba Da Zama A Manchester City – Guadiola

Next Post

Za Mu Bai Wa Masu Zanga-zanga Kariya Idan Ta Lumana Ce – Sufeton ‘Yansanda

Related

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

7 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

13 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

15 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

17 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

19 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

1 day ago
Next Post
Za Mu Bai Wa Masu Zanga-zanga Kariya Idan Ta Lumana Ce – Sufeton ‘Yansanda

Za Mu Bai Wa Masu Zanga-zanga Kariya Idan Ta Lumana Ce - Sufeton 'Yansanda

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.