ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Ba Na Cikin Gwamnati Ba Zan Shiga Zanga-zanga Ba – Abdulaziz Abdulaziz

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Zanga-zanga

Mai taimaka wa shugaban ƙasa a kan kafafen yada labarai, Abdulaziz Abdulaziz, ya bayyana cewa ko baya cikin gwamnatin Bola Tinubu, ba zai shiga zanga-zangar da ake kokarin yi a watan Agusta ba. 

Abdulaziz, ya bayyana haka ne a shafinsa Facebook a safiyar yau Laraba, inda ya mayarwa da waɗanda suke nemo tsofaffin rubuce-rubucensa na baya da ya yi na shiga zanga-zanga.

  • Babu Tabbacin Ko Ederson Zai Ci Gaba Da Zama A Manchester City – Guadiola
  • Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin ‘Yan Matan Chibok

Ya ce “Masu tone-tonen tsoffin rubutuna ba sai kun ba wa kanku wahala ba!

ADVERTISEMENT

“Na shiga zanga-zanga guda biyu a baya. Na shiga ta cire tallafin man fetur a 2012 a Kano na kuma shiga ta ‘Bring Back Our Girls’ a Abuja a 2014. Duka wadancan zanga-zanga suna da tsari da shugabanci da kuma sanin inda aka dosa.

Yawanci kafin fita zanga-zanga ana fitar da tsarin yadda za ta gudana da kuma irin abin da masu zanga-zangar suke buƙata, hakan ya sa Abdulaziz ya ce wannan ba ta da tsarin da ya kamata a shiga.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

“Amma a 2019 ban shiga zanga-zangar ENDSARS ba saboda (kamar yadda na faɗa a wancan lokacin) ba ta da tsarin shugabanci da takamammiyar manufa (idan ban da ƙoƙarin tunzura mutane da yi wa gwamnati tawaye wadda kuma kan kai ga jefa ƙasa cikin ruɗani). Na ɗauki wannan matsayar ne duk da bani da alaƙa ta kusa ko ta nesa da gwamnatin Buhari.

“Zanga-zangar da ake shirin yi ta August b ata da bambanci da ta Endsars don haka ko da ba na cikin gwamnati ba zan taɓa goyon bayanta ba.”

Batun zanga-zanga dai shi ne abin da ake yawan tattaunawa a shafukan sada zumunta a Nijeriya a ‘yan kwanakin nan, sai dai har yanzu ba a san jagororin zanga-zangar ba.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta bakin ministan yaɗa labarai, ya roƙi matasan da suke shirya zanga-zangar da cewa su sake bashi lokaci domin ya saisaita lamuran ƙasar nan.

Sai dai tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, wanda kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa ne a jam’iyyar adawa ta PDP, ya soki gwamnatin tarayya, inda ya ce waɗanda suke cewa ka da a yi zanga-zangar su ne waɗanda suka jagoranci wadda aka yi a baya.

Zanga-zanga
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Za Mu Bai Wa Masu Zanga-zanga Kariya Idan Ta Lumana Ce – Sufeton ‘Yansanda

Za Mu Bai Wa Masu Zanga-zanga Kariya Idan Ta Lumana Ce - Sufeton 'Yansanda

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.