ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Ba Na Cikin Gwamnati Ba Zan Shiga Zanga-zanga Ba – Abdulaziz Abdulaziz

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Zanga-zanga

Mai taimaka wa shugaban ƙasa a kan kafafen yada labarai, Abdulaziz Abdulaziz, ya bayyana cewa ko baya cikin gwamnatin Bola Tinubu, ba zai shiga zanga-zangar da ake kokarin yi a watan Agusta ba. 

Abdulaziz, ya bayyana haka ne a shafinsa Facebook a safiyar yau Laraba, inda ya mayarwa da waɗanda suke nemo tsofaffin rubuce-rubucensa na baya da ya yi na shiga zanga-zanga.

  • Babu Tabbacin Ko Ederson Zai Ci Gaba Da Zama A Manchester City – Guadiola
  • Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin ‘Yan Matan Chibok

Ya ce “Masu tone-tonen tsoffin rubutuna ba sai kun ba wa kanku wahala ba!

ADVERTISEMENT

“Na shiga zanga-zanga guda biyu a baya. Na shiga ta cire tallafin man fetur a 2012 a Kano na kuma shiga ta ‘Bring Back Our Girls’ a Abuja a 2014. Duka wadancan zanga-zanga suna da tsari da shugabanci da kuma sanin inda aka dosa.

Yawanci kafin fita zanga-zanga ana fitar da tsarin yadda za ta gudana da kuma irin abin da masu zanga-zangar suke buƙata, hakan ya sa Abdulaziz ya ce wannan ba ta da tsarin da ya kamata a shiga.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

“Amma a 2019 ban shiga zanga-zangar ENDSARS ba saboda (kamar yadda na faɗa a wancan lokacin) ba ta da tsarin shugabanci da takamammiyar manufa (idan ban da ƙoƙarin tunzura mutane da yi wa gwamnati tawaye wadda kuma kan kai ga jefa ƙasa cikin ruɗani). Na ɗauki wannan matsayar ne duk da bani da alaƙa ta kusa ko ta nesa da gwamnatin Buhari.

“Zanga-zangar da ake shirin yi ta August b ata da bambanci da ta Endsars don haka ko da ba na cikin gwamnati ba zan taɓa goyon bayanta ba.”

Batun zanga-zanga dai shi ne abin da ake yawan tattaunawa a shafukan sada zumunta a Nijeriya a ‘yan kwanakin nan, sai dai har yanzu ba a san jagororin zanga-zangar ba.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta bakin ministan yaɗa labarai, ya roƙi matasan da suke shirya zanga-zangar da cewa su sake bashi lokaci domin ya saisaita lamuran ƙasar nan.

Sai dai tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, wanda kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa ne a jam’iyyar adawa ta PDP, ya soki gwamnatin tarayya, inda ya ce waɗanda suke cewa ka da a yi zanga-zangar su ne waɗanda suka jagoranci wadda aka yi a baya.

Zanga-zanga
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Zanga-zanga
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Zanga-zanga
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe
Manyan Labarai

Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

September 11, 2026
Next Post
Za Mu Bai Wa Masu Zanga-zanga Kariya Idan Ta Lumana Ce – Sufeton ‘Yansanda

Za Mu Bai Wa Masu Zanga-zanga Kariya Idan Ta Lumana Ce - Sufeton 'Yansanda

LABARAI MASU NASABA

Zanga-zanga

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris

September 11, 2026
Zanga-zanga

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu

September 11, 2026
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

September 11, 2026
Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.