• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon wanann watan ne kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta kammala kulla yarjejeniyar daukar dan wasa Kylian Mbappe, wanda kwantaraginsa ya kare a Paris St Germain a karshen 30 ga watan Yunin wannan shekarar.

Ana sa ran dan wasan mai shekara 25 a duniya zai koma Sifaniya da buga wasa a ranar 1 ga watan Yuli da zarar an bude kasuwar saye da sayar da ‘yan kwallo a La Liga. Koda yake a lokacin ana tsaka da wasannin Euro 2024, kenan za a jira kwazon da tawagar Faransa za ta yi ko za ta kai wasan karshe da za a yi ranar 14 ga watan Yuli mai zuwa.

  • Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya amsa Tambayoyin ’Yan Jaridu Game Da Sayarwa Taiwan Makamai Da Amurka Ta Yi A Sabon Zagaye
  • ‘Yansanda Sun Cafke Ɗan Banga Kan Zargin Kashe Mutum 2 Kan Rikicin Gona A Adamawa

Daga nan ne Mbappe zai dauki hutu, sai kuma ya koma Real Madrid inda kungiyar ta sanar da cewa za ta gabatar da shi a gaban magoya bayanta a filin wasa na Santiago Bernabeu a ranar 16 ga watan gobe. Tun cikin watan Fabrairu dan wasan na tawagar Faransa ya amince baka da baka da cewar zai koma Real Madrid, sannan cikin watan Mayu aka sanar da zai bar PSG a karshen kakar wasa ta 2023 zuwa 2024.

Mbappe yana da shekara 16 ya fara buga wa Monaco wasa a Disambar shekarar 2015, wanda ya doke tarihin Thierry Henry a matakin matashin da ya fara yi wa kungiyar wasa.

Sannan shi ne matashin da ke kan gaba a ci wa kungiyar kwallaye a tarihi, yayin da a kakar wasa ta 2016 zuwa 2017 yana cikin ‘yan wasan Monaco da suka kai dab da karshe a Kofin Zakarun Turai.

Labarai Masu Nasaba

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

A kuma kakar ce ya zura kwallo 15 a raga da ta kai Monaco ta lashe babban kofin gasar Ligue 1 ta Faransa sannan daga baya ya koma Paris St Germain kan kudi Yuro miliyan 180 yana da shekara 18 da haihuwa.

Tsohon dan wasan na Monaco ya lashe kofin duniya a shekarar 2018 wanda aka buga a Rasha, wanda ya zama matashi mai karancin shekaru da ya dauki kofin duniya, bayan Pele a 1958 da cin kwallo a wasan karshe.

Haka kuma Mbappe ya kai wasan karshe a gasar kofin duniya a Katar a 2022, inda Faransa ta yi rashin nasara a hannun Argentina a bugun fenariti sanann shi ne kan gaba a cin kwallaye a gasar Faransa ta Ligue 1 da aka kammala, kuma karo shida a jere yana wannan bajintar.

Ya kuma lashe Ligue 1 karo bakwai a tarihi, wanda ke fatan daukar Kofin Zakarun Turai da kuma kyautar Ballon d’Or nan gaba sai dai kafin nan yana fatan zai taimaka wa kasar ta lashe Euro 2024 da za ta buga a Jamus a bana.

Mbappe ya lashe kofin duniya a 2018, kuma shi ne kan gaba a yawan cin kwallaye a PSG mai 256 a raga, tun bayan da ya koma kungiyar aro daga Monaco a shekarar 2017.

Ya amince da yarjejeniyar da za ta kare a Real Madrid zuwa karshen kakar wasa ta 2029, sannan zai dinga karbar kudi fam miliyan 12.8 a kowacce kakar wasa a Real Madrid.

Haka kuma zai karbi karin ladan Fam miliyan 128 wato na tsarabe-tsarabe da za a biya cikin shekara biyar, kuma zai rike kudin tallace-tallacensa da zai samu daga kamfanoni daban-daban.

Idan ba a manta ba Real Madrid ce ta lashe La Liga na bana na 36 jimilla, sannan kuma Real Madrid ce ta dauki Kofin Zakarun Turai na bana na 15 jimilla, bayan da ta doke Borussia Dortmund 2-0 a wasan karshe a filin wasa na Wembley.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kwallon KafaMbappeReal Madrid
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Kano Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Kawo Karshen Fadan Daba A Kano

Next Post

Yadda Bukukuwan Sallah Suka Kasance A Garuruwanmu – Mabiya Taskira

Related

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City
Wasanni

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

9 hours ago
Boniface
Wasanni

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

2 days ago
Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong
Wasanni

Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong

3 days ago
Yadda Arsenal Ta Doke Manchester United Da Ci 1-0
Wasanni

Yadda Arsenal Ta Doke Manchester United Da Ci 1-0

5 days ago
Waye Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
Wasanni

Waye Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

6 days ago
Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?
Wasanni

Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?

6 days ago
Next Post
Yadda Bukukuwan Sallah Suka Kasance A Garuruwanmu – Mabiya Taskira

Yadda Bukukuwan Sallah Suka Kasance A Garuruwanmu - Mabiya Taskira

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.