• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon wanann watan ne kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta kammala kulla yarjejeniyar daukar dan wasa Kylian Mbappe, wanda kwantaraginsa ya kare a Paris St Germain a karshen 30 ga watan Yunin wannan shekarar.

Ana sa ran dan wasan mai shekara 25 a duniya zai koma Sifaniya da buga wasa a ranar 1 ga watan Yuli da zarar an bude kasuwar saye da sayar da ‘yan kwallo a La Liga. Koda yake a lokacin ana tsaka da wasannin Euro 2024, kenan za a jira kwazon da tawagar Faransa za ta yi ko za ta kai wasan karshe da za a yi ranar 14 ga watan Yuli mai zuwa.

  • Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya amsa Tambayoyin ’Yan Jaridu Game Da Sayarwa Taiwan Makamai Da Amurka Ta Yi A Sabon Zagaye
  • ‘Yansanda Sun Cafke Ɗan Banga Kan Zargin Kashe Mutum 2 Kan Rikicin Gona A Adamawa

Daga nan ne Mbappe zai dauki hutu, sai kuma ya koma Real Madrid inda kungiyar ta sanar da cewa za ta gabatar da shi a gaban magoya bayanta a filin wasa na Santiago Bernabeu a ranar 16 ga watan gobe. Tun cikin watan Fabrairu dan wasan na tawagar Faransa ya amince baka da baka da cewar zai koma Real Madrid, sannan cikin watan Mayu aka sanar da zai bar PSG a karshen kakar wasa ta 2023 zuwa 2024.

Mbappe yana da shekara 16 ya fara buga wa Monaco wasa a Disambar shekarar 2015, wanda ya doke tarihin Thierry Henry a matakin matashin da ya fara yi wa kungiyar wasa.

Sannan shi ne matashin da ke kan gaba a ci wa kungiyar kwallaye a tarihi, yayin da a kakar wasa ta 2016 zuwa 2017 yana cikin ‘yan wasan Monaco da suka kai dab da karshe a Kofin Zakarun Turai.

Labarai Masu Nasaba

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

A kuma kakar ce ya zura kwallo 15 a raga da ta kai Monaco ta lashe babban kofin gasar Ligue 1 ta Faransa sannan daga baya ya koma Paris St Germain kan kudi Yuro miliyan 180 yana da shekara 18 da haihuwa.

Tsohon dan wasan na Monaco ya lashe kofin duniya a shekarar 2018 wanda aka buga a Rasha, wanda ya zama matashi mai karancin shekaru da ya dauki kofin duniya, bayan Pele a 1958 da cin kwallo a wasan karshe.

Haka kuma Mbappe ya kai wasan karshe a gasar kofin duniya a Katar a 2022, inda Faransa ta yi rashin nasara a hannun Argentina a bugun fenariti sanann shi ne kan gaba a cin kwallaye a gasar Faransa ta Ligue 1 da aka kammala, kuma karo shida a jere yana wannan bajintar.

Ya kuma lashe Ligue 1 karo bakwai a tarihi, wanda ke fatan daukar Kofin Zakarun Turai da kuma kyautar Ballon d’Or nan gaba sai dai kafin nan yana fatan zai taimaka wa kasar ta lashe Euro 2024 da za ta buga a Jamus a bana.

Mbappe ya lashe kofin duniya a 2018, kuma shi ne kan gaba a yawan cin kwallaye a PSG mai 256 a raga, tun bayan da ya koma kungiyar aro daga Monaco a shekarar 2017.

Ya amince da yarjejeniyar da za ta kare a Real Madrid zuwa karshen kakar wasa ta 2029, sannan zai dinga karbar kudi fam miliyan 12.8 a kowacce kakar wasa a Real Madrid.

Haka kuma zai karbi karin ladan Fam miliyan 128 wato na tsarabe-tsarabe da za a biya cikin shekara biyar, kuma zai rike kudin tallace-tallacensa da zai samu daga kamfanoni daban-daban.

Idan ba a manta ba Real Madrid ce ta lashe La Liga na bana na 36 jimilla, sannan kuma Real Madrid ce ta dauki Kofin Zakarun Turai na bana na 15 jimilla, bayan da ta doke Borussia Dortmund 2-0 a wasan karshe a filin wasa na Wembley.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kwallon KafaMbappeReal Madrid
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Kano Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Kawo Karshen Fadan Daba A Kano

Next Post

Yadda Bukukuwan Sallah Suka Kasance A Garuruwanmu – Mabiya Taskira

Related

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

23 minutes ago
Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique
Wasanni

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

1 day ago
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense
Wasanni

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

2 days ago
Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars
Wasanni

Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars

2 days ago
Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa

2 days ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin
Wasanni

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

3 days ago
Next Post
Yadda Bukukuwan Sallah Suka Kasance A Garuruwanmu – Mabiya Taskira

Yadda Bukukuwan Sallah Suka Kasance A Garuruwanmu - Mabiya Taskira

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.