ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Mbappe

A farkon wanann watan ne kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta kammala kulla yarjejeniyar daukar dan wasa Kylian Mbappe, wanda kwantaraginsa ya kare a Paris St Germain a karshen 30 ga watan Yunin wannan shekarar.

Ana sa ran dan wasan mai shekara 25 a duniya zai koma Sifaniya da buga wasa a ranar 1 ga watan Yuli da zarar an bude kasuwar saye da sayar da ‘yan kwallo a La Liga. Koda yake a lokacin ana tsaka da wasannin Euro 2024, kenan za a jira kwazon da tawagar Faransa za ta yi ko za ta kai wasan karshe da za a yi ranar 14 ga watan Yuli mai zuwa.

  • Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya amsa Tambayoyin ’Yan Jaridu Game Da Sayarwa Taiwan Makamai Da Amurka Ta Yi A Sabon Zagaye
  • ‘Yansanda Sun Cafke Ɗan Banga Kan Zargin Kashe Mutum 2 Kan Rikicin Gona A Adamawa

Daga nan ne Mbappe zai dauki hutu, sai kuma ya koma Real Madrid inda kungiyar ta sanar da cewa za ta gabatar da shi a gaban magoya bayanta a filin wasa na Santiago Bernabeu a ranar 16 ga watan gobe. Tun cikin watan Fabrairu dan wasan na tawagar Faransa ya amince baka da baka da cewar zai koma Real Madrid, sannan cikin watan Mayu aka sanar da zai bar PSG a karshen kakar wasa ta 2023 zuwa 2024.

ADVERTISEMENT

Mbappe yana da shekara 16 ya fara buga wa Monaco wasa a Disambar shekarar 2015, wanda ya doke tarihin Thierry Henry a matakin matashin da ya fara yi wa kungiyar wasa.

Sannan shi ne matashin da ke kan gaba a ci wa kungiyar kwallaye a tarihi, yayin da a kakar wasa ta 2016 zuwa 2017 yana cikin ‘yan wasan Monaco da suka kai dab da karshe a Kofin Zakarun Turai.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

A kuma kakar ce ya zura kwallo 15 a raga da ta kai Monaco ta lashe babban kofin gasar Ligue 1 ta Faransa sannan daga baya ya koma Paris St Germain kan kudi Yuro miliyan 180 yana da shekara 18 da haihuwa.

Tsohon dan wasan na Monaco ya lashe kofin duniya a shekarar 2018 wanda aka buga a Rasha, wanda ya zama matashi mai karancin shekaru da ya dauki kofin duniya, bayan Pele a 1958 da cin kwallo a wasan karshe.

Haka kuma Mbappe ya kai wasan karshe a gasar kofin duniya a Katar a 2022, inda Faransa ta yi rashin nasara a hannun Argentina a bugun fenariti sanann shi ne kan gaba a cin kwallaye a gasar Faransa ta Ligue 1 da aka kammala, kuma karo shida a jere yana wannan bajintar.

Ya kuma lashe Ligue 1 karo bakwai a tarihi, wanda ke fatan daukar Kofin Zakarun Turai da kuma kyautar Ballon d’Or nan gaba sai dai kafin nan yana fatan zai taimaka wa kasar ta lashe Euro 2024 da za ta buga a Jamus a bana.

Mbappe ya lashe kofin duniya a 2018, kuma shi ne kan gaba a yawan cin kwallaye a PSG mai 256 a raga, tun bayan da ya koma kungiyar aro daga Monaco a shekarar 2017.

Ya amince da yarjejeniyar da za ta kare a Real Madrid zuwa karshen kakar wasa ta 2029, sannan zai dinga karbar kudi fam miliyan 12.8 a kowacce kakar wasa a Real Madrid.

Haka kuma zai karbi karin ladan Fam miliyan 128 wato na tsarabe-tsarabe da za a biya cikin shekara biyar, kuma zai rike kudin tallace-tallacensa da zai samu daga kamfanoni daban-daban.

Idan ba a manta ba Real Madrid ce ta lashe La Liga na bana na 36 jimilla, sannan kuma Real Madrid ce ta dauki Kofin Zakarun Turai na bana na 15 jimilla, bayan da ta doke Borussia Dortmund 2-0 a wasan karshe a filin wasa na Wembley.

Mbappe
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Yadda Bukukuwan Sallah Suka Kasance A Garuruwanmu – Mabiya Taskira

Yadda Bukukuwan Sallah Suka Kasance A Garuruwanmu - Mabiya Taskira

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.