ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Mbappe

A farkon wanann watan ne kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta kammala kulla yarjejeniyar daukar dan wasa Kylian Mbappe, wanda kwantaraginsa ya kare a Paris St Germain a karshen 30 ga watan Yunin wannan shekarar.

Ana sa ran dan wasan mai shekara 25 a duniya zai koma Sifaniya da buga wasa a ranar 1 ga watan Yuli da zarar an bude kasuwar saye da sayar da ‘yan kwallo a La Liga. Koda yake a lokacin ana tsaka da wasannin Euro 2024, kenan za a jira kwazon da tawagar Faransa za ta yi ko za ta kai wasan karshe da za a yi ranar 14 ga watan Yuli mai zuwa.

  • Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya amsa Tambayoyin ’Yan Jaridu Game Da Sayarwa Taiwan Makamai Da Amurka Ta Yi A Sabon Zagaye
  • ‘Yansanda Sun Cafke Ɗan Banga Kan Zargin Kashe Mutum 2 Kan Rikicin Gona A Adamawa

Daga nan ne Mbappe zai dauki hutu, sai kuma ya koma Real Madrid inda kungiyar ta sanar da cewa za ta gabatar da shi a gaban magoya bayanta a filin wasa na Santiago Bernabeu a ranar 16 ga watan gobe. Tun cikin watan Fabrairu dan wasan na tawagar Faransa ya amince baka da baka da cewar zai koma Real Madrid, sannan cikin watan Mayu aka sanar da zai bar PSG a karshen kakar wasa ta 2023 zuwa 2024.

ADVERTISEMENT

Mbappe yana da shekara 16 ya fara buga wa Monaco wasa a Disambar shekarar 2015, wanda ya doke tarihin Thierry Henry a matakin matashin da ya fara yi wa kungiyar wasa.

Sannan shi ne matashin da ke kan gaba a ci wa kungiyar kwallaye a tarihi, yayin da a kakar wasa ta 2016 zuwa 2017 yana cikin ‘yan wasan Monaco da suka kai dab da karshe a Kofin Zakarun Turai.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

A kuma kakar ce ya zura kwallo 15 a raga da ta kai Monaco ta lashe babban kofin gasar Ligue 1 ta Faransa sannan daga baya ya koma Paris St Germain kan kudi Yuro miliyan 180 yana da shekara 18 da haihuwa.

Tsohon dan wasan na Monaco ya lashe kofin duniya a shekarar 2018 wanda aka buga a Rasha, wanda ya zama matashi mai karancin shekaru da ya dauki kofin duniya, bayan Pele a 1958 da cin kwallo a wasan karshe.

Haka kuma Mbappe ya kai wasan karshe a gasar kofin duniya a Katar a 2022, inda Faransa ta yi rashin nasara a hannun Argentina a bugun fenariti sanann shi ne kan gaba a cin kwallaye a gasar Faransa ta Ligue 1 da aka kammala, kuma karo shida a jere yana wannan bajintar.

Ya kuma lashe Ligue 1 karo bakwai a tarihi, wanda ke fatan daukar Kofin Zakarun Turai da kuma kyautar Ballon d’Or nan gaba sai dai kafin nan yana fatan zai taimaka wa kasar ta lashe Euro 2024 da za ta buga a Jamus a bana.

Mbappe ya lashe kofin duniya a 2018, kuma shi ne kan gaba a yawan cin kwallaye a PSG mai 256 a raga, tun bayan da ya koma kungiyar aro daga Monaco a shekarar 2017.

Ya amince da yarjejeniyar da za ta kare a Real Madrid zuwa karshen kakar wasa ta 2029, sannan zai dinga karbar kudi fam miliyan 12.8 a kowacce kakar wasa a Real Madrid.

Haka kuma zai karbi karin ladan Fam miliyan 128 wato na tsarabe-tsarabe da za a biya cikin shekara biyar, kuma zai rike kudin tallace-tallacensa da zai samu daga kamfanoni daban-daban.

Idan ba a manta ba Real Madrid ce ta lashe La Liga na bana na 36 jimilla, sannan kuma Real Madrid ce ta dauki Kofin Zakarun Turai na bana na 15 jimilla, bayan da ta doke Borussia Dortmund 2-0 a wasan karshe a filin wasa na Wembley.

Mbappe
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Yadda Bukukuwan Sallah Suka Kasance A Garuruwanmu – Mabiya Taskira

Yadda Bukukuwan Sallah Suka Kasance A Garuruwanmu - Mabiya Taskira

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.