• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Sin Na Neman Samun Jituwa Tsakanin Dan Adam Da Muhallin Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kokarin Sin Na Neman Samun Jituwa Tsakanin Dan Adam Da Muhallin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kogin Yangtse, wani kogi ne na kasar Sin, wanda tsawonsa ya kai fiye da kilomita 6300, ko kuma mu ce kogi ne mafi tsawo na 3 a duniya.

An taba samun mutane fiye da dubu 200, da suke gudanar da aikin kamun kifi a kogin Yangtse. Amma sannu a hankali, kifayen da ke cikin kogin ya ragu, sakamakon yawan sun kifi fiye da kima, da shigar da gurbataccen ruwa cikin kogin, lamarin da ya sanya masunta cikin wani yanayi na kunci.

  • Jakadan Kasar Sin Ya Bayyana Damuwa Kan Yadda Ake Nuna Bambanci Ga ‘Yan Kananan Kabilu Yayin Da Ake Aiwatar Da Doka A Wasu Kasashe

Sai dai daga bisani, an fara aiwatar da wata doka ta tsawon shekaru 10, ta hana kamun kifi a kogin Yangtse, tun daga ranar 1 ga watan Janairun shekarar 2021, a matsayin daya daga cikin matakan da kasar ke dauka, da zummar kare muhallin yankin kogin Yangtse, da kyautata zaman rayuwar mutane masu ruwa da tsaki.

Gwamnatin kasar Sin ta taimaki masunta fiye da dubu 200, wajen samun sabbin guraben aikin yi a sauran sana’o’i daban daban.

Kana daga cikinsu, mutanen da suka tsufa, an ba su damar yin ritaya, inda ake samar musu da kudin fensho na tsofaffi a duk wata, don tabbatar da ingancin rayuwarsu.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

A sa’i daya kuma, ana ta samun ci gaba a kokarin kare muhallin yankin kogin Yangtse, inda ake samun ruwa mai tsabta, da karin kifaye.

Yadda aka kyautata muhallin yankin kogin Yangtse, ya nuna wani abun da Sinawa suka dora muhimmanci a kai, yayin da suke neman zamanintar da kasarsu, wato kokarin neman samun jituwa tsakain dan Adam da muhalli.

Ana kokarin raya tattalin arzikin kasa ne don kyautata zaman rayuwar jama’arta, kana ba a taba raba zaman rayuwa mai inganci da muhalli mai kyau ba. Sai dai ta yaya ake iya raya tattalin arziki, gami da kare muhallin halittu, a lokaci guda? Tabbas, Sinawa suna kokarin gudanar da bincike da gwaje-gwaje a wannan fanni.

Akwai wani babban tabki mai suna Qiandao a gundumar Chun’an ta lardin Zhejiang dake gabashin kasar Sin. Wani wuri ne mai ni’imtaccen muhalli, da duwatsu da tabkuna masu kyan gani.

Sai dai manufar kare muhalli ta takaita damammakin da mutanen wurin suke da shi na raya masana’antu. Wannan yanayi ya sa mutanen wurin karkarta ga sauran dabaru don raya tattalin arziki.

Idan mun dauki wani kauye mai suna Xiajiang dake gundumar Chun’an a matsayin misali, muka tantance sana’ar da mazauna kauyen suka dauka wajen raya kauyen, za mu ga babbar sana’ar da suka dauka ita ce yawon shakatawa.

A cikin kauyen, kusan kowane magidanci na kula da wani karamin otel, a karkashin jagorancin hukumar kauyen. Ko da a shekarar 2020, wani lokaci da aka fi fama da mummunar illar da annobar COVID-19 ta haifar, kauyen ya janyo mutane kimanin dubu 770, wadanda suka ziyarci kauyen, tare da sayen kayayyaki, da cin abinci, da jin dadin hutunsu.

Sa’an nan, a garin Linqi dake dab da kauyen Xiajiang, mutane sun fi dora muhimmanci kan aikin dasa wasu bishiyoyi, da sarrafa su zuwa magungunan gargajiya. Yanzu wasu magungunan gargajiya guda 6 da ake samarwa a garin, suna samun karbuwa sosai a kasuwannin kasar Sin.

Ta sana’ar yawon shakatawa, da sarrafa magungunan gargajiya, ana samar da guraben aikin yi ga jama’a, da hanyoyin da ake bi wajen raya tattalin arziki, ba tare da gurbata muhalli ba.

Sa’an nan a wajen tabkin Qiandao, yadda ake kokarin kare tsabtar ruwan tabkin, ba ya nufin hana mutum cin gajiyar albarkatun da ke akwai. Wani abun da ake fitarwa daga cikin ruwan tabkin Qiandao, wanda ya fi shahara a kasuwannin kasar Sin, shi ne wani nau’in kifin da ake kira Bighead Carp.

Sinawa suna son cin naman wannan nau’in kifi sosai. Ban da haka kuma, ta hanyar kiwon kifin Bighead Carp da ake yi a tabkin, ana iya samar da gudunmowa ga kokarin tabbatar da tsabtar ruwan tabkin. Saboda kananan kifayen Bighead Carp kilo daya, su kan iya cinye kimanin kilo 40 na ciyayin ruwa na Algae mai gurbata muhalli, yayin da suke girma.

Ban da wannan kuma, yunkuri na kiyaye tsabtar ruwa bai hana su gudanar da aikin gona ba. A kauye Anyang, duk a karkashin gundumar Chun’an, ana kokarin yayata wata fasahar aikin gona ta zamani ta kare tsabtar ruwan kogi.

Ta wannan fasaha, ana daidaita nau’ikan ganyayen da ake shukawa, ta yadda ake samun damar rage yin amfani da maganin kashe kwari mai guba, da takin zamani. Ban da wannan kuma, an dasa wasu bishiyoyi na musamman a gefen gonaki, wadanda suke taimakawa wajen tace sinadarai masu guba daga cikin ruwan da ya fito daga cikin gonaki. Ta wadannan hanyoyi, an rage tasirin da aikin gona yake wa muhallin halittu kwarai da gaske.

Yayin da kasar Sin ke neman ganin samun ci gaban masana’antu, da wadatar da jama’arta, da kare muhallin halittu a lokaci guda, tana kuma son raba fasahohi masu kyau da ta samu ga sauran kasashe masu tasowa, ta yadda za a cimma burin samun ci gaba mai dorewa a kasashe daban daban.

Idan mun dauki nahiyar Afirka a matsayin wani misali. Cikin shekarun da suka gabata, kasar Sin ta dukufa wajen taimakawa kasashen Afirka wajen raya makamashi mai tsabta.

A Bangui, fadar mulkin kasar Afirka ta tsakiya, an dade ana fama da matsalar karancin wutar lantarki. A baya, magidantan birnin kimanin kashi 35% kacal ne ke samun hidimar wutar lantarki.

Sai dai a ranar 15 ga watan Yunin bana, tashar samar da wutar lantarki mai amfani da zafin rana ta Sakai, da kasar Sin ta ba da ita a matsayin tallafi ga kasar Afirka ta Tsakiya ta fara aiki. Daga bisani, kimanin kashi 2 cikin kashi 3 na daukacin magidantan birnin Bangui, sun samu damar yin amfani da wutar lantarki, lamarin da ya saukaka zaman rayuwarsu matuka.

Ban da wannan kuma, a kasar Uganda, wani kamfanin kasar Sin na ci gaba da kokarin gina tashar samar da wutar lantarki mai amfani da karfin ruwa ta Karuma. Ana shirin kaddamar da wannan tasha a watan Oktoba da muke ciki, inda za ta zama tashar samar da wutar lantarki mafi girma a kasar Uganda.

Yadda ake yin amfani da karfin ruwa maimakon makamashi na kwal wajen samar da wutar lantarki, yana taimakawa wajen kare muhalli sosai.

Ban da wannan kuma, yayin da ake gina tashar, an kebe hanyoyin da dabbobi za su bi, don magance matsalar tare musu hanyar kaura. Haka zalika, an sanya wasu manyan injuna a wani wurin dake da nisan mita 80 a karkashin kasa, don kare dazuzzuka da halittun dake doron kasa.

A ganin Sinawa, duniyarmu tamkar kauye daya ne ga daukacin bil Adama. Dalilin raya tattalin arziki, gami da kare muhallin halittu a lokaci guda, shi ne neman tabbatar da makoma mai haske ta dan Adam.

Ya kamata mu hada kai, don tabbatar da samun jituwa tsakanin dan Adam da muhallin halittu, da kiyaye hakan har abada. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Habasha Da ‘Yan Tawayen Tigray Za Su Zauna A Teburin Sulhu

Next Post

Dan Bindiga Ya Kashe Kananan Yara ‘Yan Makaranta 36 A Thailand 

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

9 minutes ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

1 hour ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

3 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

4 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

11 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

13 hours ago
Next Post
Dan Bindiga Ya Kashe Kananan Yara ‘Yan Makaranta 36 A Thailand 

Dan Bindiga Ya Kashe Kananan Yara 'Yan Makaranta 36 A Thailand 

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.