• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
Dare

Ku gafarce mu a sabili da yadda kwamitin sulhu ya kasa ceton yaran Gaza, kuma ya kasa kare mata da tsoffi da likitoci da nas nas da ‘yan jarida a Gaza…Kasashe mambobi 14 na kwamitin sun yi namijin kokari, amma sun kasa samar da taimako, sakamakon yadda Isra’ila ke samun kariya daga tsarin duniya maras daidaito. Kalaman da zaunannen wakilin kasar Aljeriya a MDD Amar Bendjama ya yi ke nan a jawabinsa, bayan da kasar Amurka ta sake kada kuri’ar rashin amincewa da wani daftarin kudurin tsagaita bude wuta a zirin Gaza a taron kwamitin sulhun da ya gudana kwanan nan, inda Mr. Amar Bendjama ya yi ta rokon gafara har sau 11.

A ranar 18 ne, kwamitin sulhun MDD ya kada kuri’a a kan wani daftarin shiri da ya bukaci a dakatar da bude wuta a Gaza nan da nan ba tare da sharuda ba, daga cikin kasashe mambobi 15 na kwamitin, 14 ne suka kada kuri’ar nuna amincewa, a yayin da kasar Amurka wadda ke da kujerar dindindin a kwamitin ta hau kujerar na ki, matakin da ya sa aka kasa zartas da kudurin. Hakan kuma ya kasance karo na shida da Amurka ta kada kuri’ar rashin amincewa da irin kudurin a kwamitin sulhun.

A jawabin da ya gabatar bayan kada kuri’ar, zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Mr. Fu Cong ya yi tambayoyi guda uku game da yadda Amurka ta hau kujerar na ki yadda ta ga dama, wato asarorin rayuka nawa ne za su kai ga tsagaita bude wuta a Gaza? Sa’an nan, aukuwar masifofi nawa za su kai ga shigar da kayayyakin jin kai Gaza ba tare da matsala ba? Sai kuma zuwa yaushe ne kwamitin sulhu zai kai ga gudanar da aikin da ya wajaba?

Shekaru kusan biyu ke nan da barkewar rikici a Gaza, rikicin da ya haifar da mummunan yanayin jin kai. Kwamitin sulhun ya yi ta yin kokari, amma Amurka ta zama karfen kafa ta hana. Idan ba mu manta ba, karon farko da Amurka ta kada kuri’ar rashin amincewa a watan Oktoban shekarar 2023, rikicin ya halaka mutane kusan 3000. A lokacin da Amurka ta sake kada kuri’ar a wannan karo, adadin mamata a sanadin rikicin ya karu har zuwa sama da dubu 65.

MDD da aka kafa bayan yakin duniya na biyu a kimanin shekaru 80 da suka gabata, yana daukar burin bai daya na bil Adam game da wanzar da zaman lafiya da ci gaba a duniya, wadda ta bude sabon babin tsarin jagorancin duniya a lokacin. Amma yadda Amurka ta hana kwamitin sulhu daukar matakai da kuma kare aniyarta ta kare aikace-aikacen da suka saba wa kudurin kwamitin sulhu, ya sa kwamitin sulhun gaza taka rawar gani a kan batun Gaza. Taron da aka gudanar a wannan karo ya kasance na 10,000 ga kwamitin sulhun, wanda ya kamata ya zama sabon babin MDD na kiyaye zaman lafiya a duniya, amma a maimakon haka, kuri’ar da Amurka ta kada ta tono mana matsalolin da MDD ke fuskanta ta fannin tsarin jagorancin duniya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Sabo da irin mawuyacin halin da ake ciki ta fannin tsarin jagorancin duniya musamman a daidai wannan lokaci, ya sa shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar inganta tsarin jagorancin duniya a kwanakin baya, shawarar da ta yi nuni da cewa, ya kamata a tsaya tsayin daka a kan kin yarda da daukar matakai na kashin kai, tare da kiyaye matsayin MDD, don ta taka rawar da ba wanda zai iya maye gurbinta a cikin tsarin jagorancin duniya. Lallai kasar Sin ta gabatar da shawarar, musamman don neman dakile ayyukan nuna fin karfi da ake fama da su a duniya, tare da samar da mafita ga kasa da kasa da suka shiga duhu.

A sati mai zuwa, za a gudanar da babbar muhawara da ma babban taron tabbatar da shirin samar da kasashe biyu a yayin babban zauren MDD, kafin haka, manyan kawayen Amurka irinsu Birtaniya da Faransa cewa suka yi za su amince da kafuwar kasar Palasdinu, lamarin da ya sake shaida cewa, babu wanda zai iya hana adalci. Lokacin da Amurka ta kada kuri’ar nuna rashin amincewa, ba yarjejeniyar zaman lafiya kadai ta jefa cikin kwadon shara ba, har da matsayinta na jagorancin duniya.

Tabbas “komai nisan dare gare zai waye”, duk duhun da Gaza ke ciki, haske zai bayyana. Fatan kasa da kasa na wanzar da zaman lafiya zai kai ga kawar da dukkan abubuwan da ke tarnaki tare da shimfida dauwamammen zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya, wanda hakan zai bude mana sabon babin tsarin jagorancin duniya.

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi
Manyan Labarai

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Next Post
SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook

SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook

LABARAI MASU NASABA

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.