ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Dare

Ku gafarce mu a sabili da yadda kwamitin sulhu ya kasa ceton yaran Gaza, kuma ya kasa kare mata da tsoffi da likitoci da nas nas da ‘yan jarida a Gaza…Kasashe mambobi 14 na kwamitin sun yi namijin kokari, amma sun kasa samar da taimako, sakamakon yadda Isra’ila ke samun kariya daga tsarin duniya maras daidaito. Kalaman da zaunannen wakilin kasar Aljeriya a MDD Amar Bendjama ya yi ke nan a jawabinsa, bayan da kasar Amurka ta sake kada kuri’ar rashin amincewa da wani daftarin kudurin tsagaita bude wuta a zirin Gaza a taron kwamitin sulhun da ya gudana kwanan nan, inda Mr. Amar Bendjama ya yi ta rokon gafara har sau 11.

A ranar 18 ne, kwamitin sulhun MDD ya kada kuri’a a kan wani daftarin shiri da ya bukaci a dakatar da bude wuta a Gaza nan da nan ba tare da sharuda ba, daga cikin kasashe mambobi 15 na kwamitin, 14 ne suka kada kuri’ar nuna amincewa, a yayin da kasar Amurka wadda ke da kujerar dindindin a kwamitin ta hau kujerar na ki, matakin da ya sa aka kasa zartas da kudurin. Hakan kuma ya kasance karo na shida da Amurka ta kada kuri’ar rashin amincewa da irin kudurin a kwamitin sulhun.

A jawabin da ya gabatar bayan kada kuri’ar, zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Mr. Fu Cong ya yi tambayoyi guda uku game da yadda Amurka ta hau kujerar na ki yadda ta ga dama, wato asarorin rayuka nawa ne za su kai ga tsagaita bude wuta a Gaza? Sa’an nan, aukuwar masifofi nawa za su kai ga shigar da kayayyakin jin kai Gaza ba tare da matsala ba? Sai kuma zuwa yaushe ne kwamitin sulhu zai kai ga gudanar da aikin da ya wajaba?

ADVERTISEMENT

Shekaru kusan biyu ke nan da barkewar rikici a Gaza, rikicin da ya haifar da mummunan yanayin jin kai. Kwamitin sulhun ya yi ta yin kokari, amma Amurka ta zama karfen kafa ta hana. Idan ba mu manta ba, karon farko da Amurka ta kada kuri’ar rashin amincewa a watan Oktoban shekarar 2023, rikicin ya halaka mutane kusan 3000. A lokacin da Amurka ta sake kada kuri’ar a wannan karo, adadin mamata a sanadin rikicin ya karu har zuwa sama da dubu 65.

MDD da aka kafa bayan yakin duniya na biyu a kimanin shekaru 80 da suka gabata, yana daukar burin bai daya na bil Adam game da wanzar da zaman lafiya da ci gaba a duniya, wadda ta bude sabon babin tsarin jagorancin duniya a lokacin. Amma yadda Amurka ta hana kwamitin sulhu daukar matakai da kuma kare aniyarta ta kare aikace-aikacen da suka saba wa kudurin kwamitin sulhu, ya sa kwamitin sulhun gaza taka rawar gani a kan batun Gaza. Taron da aka gudanar a wannan karo ya kasance na 10,000 ga kwamitin sulhun, wanda ya kamata ya zama sabon babin MDD na kiyaye zaman lafiya a duniya, amma a maimakon haka, kuri’ar da Amurka ta kada ta tono mana matsalolin da MDD ke fuskanta ta fannin tsarin jagorancin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Sabo da irin mawuyacin halin da ake ciki ta fannin tsarin jagorancin duniya musamman a daidai wannan lokaci, ya sa shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar inganta tsarin jagorancin duniya a kwanakin baya, shawarar da ta yi nuni da cewa, ya kamata a tsaya tsayin daka a kan kin yarda da daukar matakai na kashin kai, tare da kiyaye matsayin MDD, don ta taka rawar da ba wanda zai iya maye gurbinta a cikin tsarin jagorancin duniya. Lallai kasar Sin ta gabatar da shawarar, musamman don neman dakile ayyukan nuna fin karfi da ake fama da su a duniya, tare da samar da mafita ga kasa da kasa da suka shiga duhu.

A sati mai zuwa, za a gudanar da babbar muhawara da ma babban taron tabbatar da shirin samar da kasashe biyu a yayin babban zauren MDD, kafin haka, manyan kawayen Amurka irinsu Birtaniya da Faransa cewa suka yi za su amince da kafuwar kasar Palasdinu, lamarin da ya sake shaida cewa, babu wanda zai iya hana adalci. Lokacin da Amurka ta kada kuri’ar nuna rashin amincewa, ba yarjejeniyar zaman lafiya kadai ta jefa cikin kwadon shara ba, har da matsayinta na jagorancin duniya.

Tabbas “komai nisan dare gare zai waye”, duk duhun da Gaza ke ciki, haske zai bayyana. Fatan kasa da kasa na wanzar da zaman lafiya zai kai ga kawar da dukkan abubuwan da ke tarnaki tare da shimfida dauwamammen zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya, wanda hakan zai bude mana sabon babin tsarin jagorancin duniya.

 

 

Dare
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Dare
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook

SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.