• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta kira ɓangarorin jami’an tsaro zuwa taron gaggawa domin tattauna hanyoyin hana ci gaba da cinna wa ofisoshin hukumar zaɓe wuta.

Taron wanda Kakakin Yaɗa Labarai na INEC, Festus Okoye ya sanar cewa ya gudana a ranar Juma’a, an tattauna matsalar hare-haren da aka kai ne sau biyu a cikin kwanaki biyu jere a jihohin Ogun da Osun.

  • Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

Okoye ya ce an gayyaci dukkan ɓangarorin da ke cikin Kwamitin Kula da Harkokin Tsaron Zaɓe (ICCES) domin tattauna matsalar, ganin yadda ranakun fara zaɓen sai kusantowa su ke yi.

“Mun samu labarin hare-haren banka wa ofisoshin INEC wuta har wurare biyu a jihohin Ogun da Osun. Wannan abu kuwa abin damuwa ne matuƙa.

INEC

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

“Kwamishinan Zaɓe na Jihar Ogun, Niyi Ijalaiye ya sanar da cewa an kai wa ofishin INEC da ke Ƙaramar Hukumar Abeokuta ta Kudu harin da aka banka masa wuta.

“Maharan sun cimma mummunan burin su bayan sun fi ƙarfin jami’an tsaron da ke wurin, inda su ka banka wa ginin wuta.

“Daga cikin kayayyakin da aka yi asara akwai akwatin zaɓe 904, rumfar shiga a yi zaɓe 29, jakunkunan zuba kayan zaɓe 57, janareto takwas da kuma katin shaidar rajistar zaɓe 65,699 na waɗanda ba su kai ga karɓar na su ba,” inji Okoye.

Haka kuma ya ƙara da cewa an yi irin wannan harin banka wa ofishin INEC wuta a ranar Alhamis, “a Karamar Hukumar Ede ta Kudu, cikin Jihar Osun, kamar yadda Kwamishinan Zaɓe na Jihar, Mutiu Agboke ya sanar.”

Sai dai ya ce a nan ɓarnar ba ta yi muni ba kamar ta Jihar Ogun. Kuma ya ce a wannan ba a ƙone muhimman takardu da katin shaidar rajistar zaɓe, kamar yadda aka yi a Ogun ba.

Yayin da ake saura kwanaki 106 a fara zaɓe, Okoye ya ce tuni INEC ta fara aikawa da kayan zaɓe a ofisoshin ta jihohi daban-daban a ƙasar nan. Dalilin haka ne ya bayyana cewa hare-haren da aka fara kaiwa har ana banka wa ofishin da ake ajiyar kayan zaɓe wuta, abin damuwa ne kuma abin takaici.

Rahotanni da dama sun bayyana yadda aka yi amfani da sunƙin biredi aka babbake ofishin INEC a Ogun.

Kwana ɗaya kuma bayan harin Ogun, wasu taƙadarai sun banka wa ofishin INEC wuta a jihar Osun.

INEC

Wasu cikakkun ‘yan ta-kife sun bi daren Laraba, kafin wayewar garin Alhamis, su ka banka wa ofishin Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) wuta, a Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun.

Ofishin da aka banka wa wutar ya na kusa da Iyaka ‘Mortuary’, cikin Ƙaramar Hukumar Abeokuta ta Kudu. ‘Yan ta-kifen da su ka banka masa wuta sun riƙa jiƙa sunƙin biredi cikin fetur, su na wurgawa a ofishin, sannan su ka ƙyasta wuta su ka tsere.

Mai gadin ofishin mai suna Azeez Hamzat, ya shaida cewa bayan an banka wutar, ya yi gaggawar kiran ‘yan sanda.

Majiya ta tabbatar cewa wasu kayayyaki da dama sun ƙone ƙurmus kafin jami’an kashe gobara su kai ɗauki.

Wakilin mu ya gano daga cikin ofisoshin da su ka ƙone, akwai ɗakin ajiyar kayayyaki, Ɗakin Yin Rajista, Zauren Shirya Taruka da sauran wasu wurare.

Kwamishinan Zaɓe na Jihar Ogun, Niyi Iyalaye ya tabbatar wa wakilin mu da wannan lamari da ya ce abin mamaki da takaici ne matuƙa.

“Amma dai yanzu mun kai rahoto wurin ‘yan sanda, kuma su na bincike,” inji shi.

Kakakin ‘Yan Sandan Jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi ya ce bai san da labarin ba, saboda bai ƙarasa ofis ba tukunna. Amma idan ya ƙarasa ya natsu, zai yi ƙarin bayani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dinkin Duniya Ta Koka Kan Rashin Tallafa Wa Mata Manoma A Nijeriya

Next Post

Firaministan Sin Ya Gana Da Shugabar Asusun IMF

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

5 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

6 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

7 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

8 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

9 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

10 hours ago
Next Post
Firaministan Sin Ya Gana Da Shugabar Asusun IMF

Firaministan Sin Ya Gana Da Shugabar Asusun IMF

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.