• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Dakatar da JAMB Daga Hana Ɗalibai Ƴan Ƙasa Da Shekaru 16 Shiga Jami’a

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
in Ilimi
0
Kotu Ta Dakatar da JAMB Daga Hana Ɗalibai Ƴan Ƙasa Da Shekaru 16 Shiga Jami’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar Kotun jihar Delta da ke Warri ta bayar da umarnin dakatar da hukumar shirya Jarrabawar shiga manyan makarantu (JAMB) daga aiwatar da sabuwar dokarta da ta kayyade shekarun shiga jami’a zuwa 16, har sai an kammala sauraron ƙarar da ake gabatarwa.

Wannan hukunci ya ƙalubalanci matakin da JAMB ta ɗauka a ranar 16 ga Oktoba, inda ta bayyana cewa duk wanda zai shiga jami’a dole ya kasance ya kai shekara 16 zuwa watan Agusta 2025.

  • JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
  • JAMB Ta Zabge Kuɗin Rajistar UTME Ga Masu Buƙata Ta Musamman

Dokar ta kasance wani ɓangare na shirin ma’aikatar Ilimi da ke son saita shekara 18 a matsayin mafi ƙanƙanta na shiga jami’a, duk da cewa JAMB ta ba da wa’adi na shekara guda ga ɗaliban zangon karatu na 2024/2025.

Sai dai, John Aikpokpo-Martins, tsohon shugaban ƙungiyar lauyoyi ta Nijeriya reshen Warri, ya shigar da ƙara a madadin ɗalibai da aka haifa tsakanin Satumba 1 zuwa Disamba 31, 2009, waɗanda suka ci jarrabawar JAMB a bana. An zargi JAMB da Jami’ar Edwin Clark a matsayin waɗanda ake ƙara.

Mai shari’a Anthony Akpovi ya amince da roƙon da Aikpokpo-Martins ya gabatar, wanda ya haɗa da umarnin dakatar da JAMB daga aiwatar da dokar kayyade shekarun da kuma tabbatar da cewa ɗiyar mai ƙarar, Angel Aikpokpo-Martins, za ta ci gaba da samun damar shiga jami’ar har sai an kammala sauraron ƙarar gaba ɗaya.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

Wannan hukunci zai ba wa waɗanda dokar ta shafa damar shiga jami’a har zuwa lokacin yanke hukunci na ƙarshe kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EducationJambSchools
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsautsayi: Ƴan Jari Bola 7 Sun Mutu A Abuja

Next Post

Mace Ta Zama Shugabar Ƙaramar Hukuma A Kano

Related

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

1 day ago
Lambar Yabo Ta CON: Buni Ya Zama Zinare Bashi Da Maboya
Ilimi

NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

7 days ago
Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta
Ilimi

Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta

7 days ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

2 weeks ago
Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima
Ilimi

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

3 weeks ago
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah
Ilimi

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

1 month ago
Next Post
Mace Ta Zama Shugabar Ƙaramar Hukuma A Kano

Mace Ta Zama Shugabar Ƙaramar Hukuma A Kano

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.