• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Hana Ganduje Ciyo Bashin Biliyan 10 Don Sanya CCTV a Kano

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotu Ta Hana Ganduje Ciyo Bashin Biliyan 10 Don Sanya CCTV a Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babban kotun tarayya da ke zamanta a Jihar Kano, ta dakatar da gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, na neman ciyo bashin naira biliyan 10 domin aikin dasa na’urorin CCTV a Jihar.

Mai Shari’a Abdullahi Liman a ranar Juma’a ya amince da rokon kungiyoyin fararen hula da aka fi sani da ‘Kano First Forum’ (KFF), cewa dole ne a kula da matakin da ake ciki dangane basuka da suke akwai.

  • Mataimakin Gwamnan Bauchi Ya Karyata Yin Murabus Daga Mukaminsa
  • Za A Kammala Babbar Hanyar Kaduna-Zariya Cikin Wata 6 Masu Zuwa — Gwamnati

Kungiyar a ranar 27 ga watan Yuni ta shigar da kara bisa matsa kaimin Darakta-Janar na kungiyar, Dakta Yusuf Isyaka-Rabiu, inda suke adawa da matakin ciwo bashin bisa dalilin cewa ba a bi ka’idojin ciwo basukan ba.

KFF ta bakin lauyoyinsu karkashin jagorancin Badamasi Suleiman-Gandu, sun roki kotun da ta dakatar da Ganduje daga cikin sabon bashin biliyan 10 da ya ke son yi.

Sauran wadanda ake kara a wannan batun sun hada da babban Antoni-Janar na jihar, Kwamishinan kudi, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar.

Labarai Masu Nasaba

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

Sauran su ne: Bankin Access, Ma’aikatar Kudi ta Tarayya, Ofishin Kula da Bashi (DMO) da Hukumar Kula da Kudi (FRC).

Mai Shari’a Abdullahi Liman, ya umarci a mika wa ma’aikatar kudi ta tarayya, ofishin kula da basuka (DMO), hukumar kula da kashe kudade ta (FRC) umarnin da kotun ta bayar na dakatar da jihar daga ciyo bashin.

KFF ta dukufa adawa da ciwo bashin ne bisa dalilinta na cewa ba a bi ka’idojin da dokokin harkalla da lamuran basuka ba.

Ranar da za a ci gaba da sauraron karar za a sanar da dukkanin bangarorin da abun ya shafa.

LEADERSHIP ta labarto cewa a ranar 15 ga watan Yuni Majalisar Dokokin Jihar, ta amince da bukatar gwamna Ganduje na ciwo bashin biliyan 10 daga bakin Access domin gudanar da aikin dasa na’urorin daukan hotuna ta CCTV.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlkaliBashiCCTVGandujeHukuncikanoKungiyaLauyoyiShari'a
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakin Gwamnan Bauchi Ya Karyata Yin Murabus Daga Mukaminsa

Next Post

‘Yandaba 45 Za Su Gurfana A Kotun Kano

Related

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

7 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

10 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

14 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

17 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

1 day ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

1 day ago
Next Post
‘Yandaba 45 Za Su Gurfana A Kotun Kano

‘Yandaba 45 Za Su Gurfana A Kotun Kano

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.