Wata babbar kotun jihar Kano a ranar Talata, ta hana jam’iyyun siyasa 19 daukar duk wani mataki da zai kawo cikas ko Tangarɗa ga zaben kananan hukumomin jihar da ke tafe.
Hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano, KANSIEC, ta hannun lauyanta Rilwanu Umar, ta shigar da karar ne mai kwanan wata, 20 ga Satumba.
- Hadimin Tinubu Ya Raba Kayayyakin Makaranta Ga Daliban Firamare A Kano
- Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Kawance Da Na Wasanni Na Matasan Sin Da Amurka
KANSIEC na neman kotu da ta hana wadanda ake kara kawo cikas ga harkokin zabe a kananan hukumomi 44 da ke jihar.
Wadanda ake kara, sun hada da jam’iyyun AP, AA, ADP, ADC, APC, APM, APGA, BP da LP.
Sauran sun hada da NRM, NNPP, PDP, PRP, SDP, YPP, YP da ZLP.
Mai shari’a Sunusi Ado-Ma’aji, ya bayar da umarnin wucin gadi da ya hana wadanda ake kara yin duk wani mataki da zai hana KANSIEC gudanar da aikinta wanda doka ta tanadar mata.
Ado-Ma’aji ya ɗage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 10 ga Oktoba, domin ci gaba da sauraron karar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp