• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Tabbatar Da Kefas A Matsayin Gwamnan Taraba

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Kefas

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan Jihar Taraba da ke zamanta a Jalingo, a ranar Asabar, ta tabbatar da Agbu Kefas na jam’iyyar PDP a matsayin halastaccen gwamnan Jihar Taraba 

Dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP, Farfesa Sani Yahaya da jam’iyyarsa ne suka garzaya kotun domin kalubalantar nasarar Kefas da PDP.

  • Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke
  • Nijeriya Ce Kasa Ta 40 A Duniya Wajen Iya Kwallon Kafa, Cewar FIFA

Mai korafin ya je kotun ne da zargin cewa zaben gwamnan da ya gudana a ranar 18 ga watan Maris cike yake da aringizun kuri’u, magudi, dangwala kuri’u fiye da kima, rashin bin dokokin zabe da INEC ba ta yi ba, tare da zargin cewa an karkatar da kuri’u da dama da NNPP ta samu zuwa ga Kefas da PDP.

Don haka ne NNPP ta bukaci kotun da ta soke nasarar Kefas tare da ayyana shi a matsayin halastaccen gwamnan Jihar ba wai Kefas ba.

Sai dai kotun Mai alkalai uku karkashin jagorancin Justice GA Sumonu, ta kori karar bisa dalilin cewa masu korafin sun gaza tabbatar da ikirarin da suke yi.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

“Masu korafin sun kasa tabbatar ma wannan kotu mai daraja cikakken bayanin yadda aka yi magudi a zaben kuma da gaza bayar da dalilin menene ya sa za a ayyana dan takarar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben Gwamnan na ranar 18 ga watan Maris

“Tun da mai korafin ya kasa tabbatar da batun aringizun kuri’u, an kori wannan karar bisa rashin sahihanci,” kotun ta yanke.

Lauyan Farfesa Sani Yahaya ya ki cewa komai bayan hukuncin. Yayin da shi kuma gwamna Kefas ya misalta nasarar tasa a matsayin burin al’ummar jihar ne ya sake cika.

Gwamnan wanda ya yi magana ta bakin kakakinsa, Emmanuel Bello, ya bukaci al’ummar jihar da su rungumi hukuncin hannun biyu-biyu, ya misalta da yin Allah ne.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Next Post
Yadda Aka Samu Jihohi 36 A Nijeriya

Yadda Aka Samu Jihohi 36 A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.