• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Za Ta Yanke Hukuncin Shari’ar Zaben Gwamnan Sakkwato A Satumba

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
2 years ago
Kotu

Kotun sauraren shari’ar zaben Gwamnan Jihar Sakkwato za ta yanke hukuncin shari’ar zaben a watan Satumba a shari’ar da Sa’idu Umar da Jam’iyyar PDP suka shigar na kalubalantar zaben Gwamna Ahmed Aliyu Sokoto na jam’iyyar APC.

Bayan saurare tare da karbar rubutattun hujjojin karshe daga dukkanin bangarori a ranar Asabar, tawagar alkalai uku a karkashin jagorancin Haruna Mshelia sun adana ranar yanke hukuncin wanda suka ce za a bayyana ranar a cikin watan Satumba.

  • Shugaban Burundi: Sin Tana Son Hada Kai Da Kasar Burundi
  • APC A Jihar Kano Za Ta Yi Taron Addu’a Don Neman Nasara A Kotu

Mai kara, Sa’idu Umar da jam’iyyar PDP suna kalubalantar zaben Gwamna Ahmed Aliyu da Mataimakinsa, Idris Muhammad Gobir na jam’iyyar APC a bisa ga rashin takardu da sabawa dokokin zabe a zaben Gwamna na 18 ga watan Maris.

A zaman kotun, jagoran lauyoyin masu kara, Aare Olumuyiwa Akinboro SAN ya bukaci kotun da ta yi la’akari da hujjoji da shaidun da suka gabatar daga wakilan jam’iyya wadanda suka tabbatar da sabawa dokokin a zaben wanda aka gudanar cike da tashin hankali.

Akinboro ya ce musamman hujjojin da suka gabatar wadanda suka nuna bambace- bambance a tsakanin satifiket din makarantar sakandire ta Gwamna Aliyu da na jami’a wadanda sun bambanta da wadanda ya gabatar a Hukumar Zabe.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

Lauyan ya kuma bukaci kotun da ta yi la’akari da kundin rajistar makarantar Town Primary School, Sabon- Birni daga 1986 -1987 da kuma takarda daga makarantar.

Ya yi bayanin dukkanin makarantun da ke da rajsita a Karamar Hukumar Sabon-Birni daga Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da Hukumar Ilimi da sauran hujjojin da ya bukaci kotun ta yi nazari.

Ya ce babu wani bayanan Gwamnati da ya nuna akwai wata makaranta mai suna Town Primary School kamar yadda Gobir ya ce ita ce makarantar da ya kammala kuma ta bashi satifiket.

Haka ma Akinboro ya bayyana cewar masu kara sun yi kokarin gamsar da kotu da hujjoji ta yadda shaidu 32 da suka kunshi jami’an Hukumar Zabe, Shugaban jam’iyyar PDP, shugaban makamai na Town Primary School Sabon-Birni da sauransu sun bayyana a gaban kotun sun kuma gabatar da takardu.

Ya ce a bisa ga hujjojin da suka gabatar, masu kariyar ba su cancanta da shiga zaben ba a bisa ga rashin takardu, don haka an yi kuskuren ba su kuri’u. A kan wannan ya bukaci kotun da ta yi watsi da kuri’un Ahmed Aliyu ta kuma tabbatar da Sa’idu Umar a matsayin wanda ya samu nasara a zaben Gwamna na 18 ga Maris 2023.

Shi kuwa lauyan APC, Hassan Liman SAN ya kalubalanci batun bambancin suna wanda ya ce ba ya hana dan takara shiga zabe don haka a cewarsa tsara sunan Gwamna Aliyu ba illa ba ce a takardunsa.

Lauyan ya bukaci kotun da ta yi watsi da karar tare da tabbatar da zaben Gwamna Ahmed Aliyu da Mataimakinsa Idris Gobir.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Next Post
Kasashen Dake Kewayen Tekun Pasifik Suna Da Ikon Neman Diyya Daga Gwamnatin Japan Kan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ruwa Cikin Teku

Kasashen Dake Kewayen Tekun Pasifik Suna Da Ikon Neman Diyya Daga Gwamnatin Japan Kan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ruwa Cikin Teku

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.