• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Za Ta Yanke Hukuncin Shari’ar Zaben Gwamnan Sakkwato A Satumba

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
2 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohowar Shugaban Kotun Gargajiya A Benue
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun sauraren shari’ar zaben Gwamnan Jihar Sakkwato za ta yanke hukuncin shari’ar zaben a watan Satumba a shari’ar da Sa’idu Umar da Jam’iyyar PDP suka shigar na kalubalantar zaben Gwamna Ahmed Aliyu Sokoto na jam’iyyar APC.

Bayan saurare tare da karbar rubutattun hujjojin karshe daga dukkanin bangarori a ranar Asabar, tawagar alkalai uku a karkashin jagorancin Haruna Mshelia sun adana ranar yanke hukuncin wanda suka ce za a bayyana ranar a cikin watan Satumba.

  • Shugaban Burundi: Sin Tana Son Hada Kai Da Kasar Burundi
  • APC A Jihar Kano Za Ta Yi Taron Addu’a Don Neman Nasara A Kotu

Mai kara, Sa’idu Umar da jam’iyyar PDP suna kalubalantar zaben Gwamna Ahmed Aliyu da Mataimakinsa, Idris Muhammad Gobir na jam’iyyar APC a bisa ga rashin takardu da sabawa dokokin zabe a zaben Gwamna na 18 ga watan Maris.

A zaman kotun, jagoran lauyoyin masu kara, Aare Olumuyiwa Akinboro SAN ya bukaci kotun da ta yi la’akari da hujjoji da shaidun da suka gabatar daga wakilan jam’iyya wadanda suka tabbatar da sabawa dokokin a zaben wanda aka gudanar cike da tashin hankali.

Akinboro ya ce musamman hujjojin da suka gabatar wadanda suka nuna bambace- bambance a tsakanin satifiket din makarantar sakandire ta Gwamna Aliyu da na jami’a wadanda sun bambanta da wadanda ya gabatar a Hukumar Zabe.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

Lauyan ya kuma bukaci kotun da ta yi la’akari da kundin rajistar makarantar Town Primary School, Sabon- Birni daga 1986 -1987 da kuma takarda daga makarantar.

Ya yi bayanin dukkanin makarantun da ke da rajsita a Karamar Hukumar Sabon-Birni daga Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da Hukumar Ilimi da sauran hujjojin da ya bukaci kotun ta yi nazari.

Ya ce babu wani bayanan Gwamnati da ya nuna akwai wata makaranta mai suna Town Primary School kamar yadda Gobir ya ce ita ce makarantar da ya kammala kuma ta bashi satifiket.

Haka ma Akinboro ya bayyana cewar masu kara sun yi kokarin gamsar da kotu da hujjoji ta yadda shaidu 32 da suka kunshi jami’an Hukumar Zabe, Shugaban jam’iyyar PDP, shugaban makamai na Town Primary School Sabon-Birni da sauransu sun bayyana a gaban kotun sun kuma gabatar da takardu.

Ya ce a bisa ga hujjojin da suka gabatar, masu kariyar ba su cancanta da shiga zaben ba a bisa ga rashin takardu, don haka an yi kuskuren ba su kuri’u. A kan wannan ya bukaci kotun da ta yi watsi da kuri’un Ahmed Aliyu ta kuma tabbatar da Sa’idu Umar a matsayin wanda ya samu nasara a zaben Gwamna na 18 ga Maris 2023.

Shi kuwa lauyan APC, Hassan Liman SAN ya kalubalanci batun bambancin suna wanda ya ce ba ya hana dan takara shiga zabe don haka a cewarsa tsara sunan Gwamna Aliyu ba illa ba ce a takardunsa.

Lauyan ya bukaci kotun da ta yi watsi da karar tare da tabbatar da zaben Gwamna Ahmed Aliyu da Mataimakinsa Idris Gobir.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Burundi: Sin Tana Son Hada Kai Da Kasar Burundi

Next Post

Kasashen Dake Kewayen Tekun Pasifik Suna Da Ikon Neman Diyya Daga Gwamnatin Japan Kan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ruwa Cikin Teku

Related

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

36 minutes ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

56 minutes ago
Amcon
Labarai

Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi

1 hour ago
Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno
Labarai

Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

2 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta YaÆ™i Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi
Da É—umi-É—uminsa

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta YaÆ™i Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

4 hours ago
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma

4 hours ago
Next Post
Kasashen Dake Kewayen Tekun Pasifik Suna Da Ikon Neman Diyya Daga Gwamnatin Japan Kan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ruwa Cikin Teku

Kasashen Dake Kewayen Tekun Pasifik Suna Da Ikon Neman Diyya Daga Gwamnatin Japan Kan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ruwa Cikin Teku

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

July 25, 2025
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

July 25, 2025
Amcon

Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi

July 25, 2025
Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

July 25, 2025

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

July 25, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta YaÆ™i Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta YaÆ™i Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

July 25, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma

July 25, 2025
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

July 25, 2025
Wutar lantarki

Arewa Maso Gabas Ce Za Ta Biya Kudin Wuta Mafi Tsada A Sabon Tsarin Lantarki

July 25, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.