ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Za Ta Yanke Hukuncin Shari’ar Zaben Gwamnan Sakkwato A Satumba

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
Kotu

Kotun sauraren shari’ar zaben Gwamnan Jihar Sakkwato za ta yanke hukuncin shari’ar zaben a watan Satumba a shari’ar da Sa’idu Umar da Jam’iyyar PDP suka shigar na kalubalantar zaben Gwamna Ahmed Aliyu Sokoto na jam’iyyar APC.

Bayan saurare tare da karbar rubutattun hujjojin karshe daga dukkanin bangarori a ranar Asabar, tawagar alkalai uku a karkashin jagorancin Haruna Mshelia sun adana ranar yanke hukuncin wanda suka ce za a bayyana ranar a cikin watan Satumba.

  • Shugaban Burundi: Sin Tana Son Hada Kai Da Kasar Burundi
  • APC A Jihar Kano Za Ta Yi Taron Addu’a Don Neman Nasara A Kotu

Mai kara, Sa’idu Umar da jam’iyyar PDP suna kalubalantar zaben Gwamna Ahmed Aliyu da Mataimakinsa, Idris Muhammad Gobir na jam’iyyar APC a bisa ga rashin takardu da sabawa dokokin zabe a zaben Gwamna na 18 ga watan Maris.

ADVERTISEMENT

A zaman kotun, jagoran lauyoyin masu kara, Aare Olumuyiwa Akinboro SAN ya bukaci kotun da ta yi la’akari da hujjoji da shaidun da suka gabatar daga wakilan jam’iyya wadanda suka tabbatar da sabawa dokokin a zaben wanda aka gudanar cike da tashin hankali.

Akinboro ya ce musamman hujjojin da suka gabatar wadanda suka nuna bambace- bambance a tsakanin satifiket din makarantar sakandire ta Gwamna Aliyu da na jami’a wadanda sun bambanta da wadanda ya gabatar a Hukumar Zabe.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Lauyan ya kuma bukaci kotun da ta yi la’akari da kundin rajistar makarantar Town Primary School, Sabon- Birni daga 1986 -1987 da kuma takarda daga makarantar.

Ya yi bayanin dukkanin makarantun da ke da rajsita a Karamar Hukumar Sabon-Birni daga Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da Hukumar Ilimi da sauran hujjojin da ya bukaci kotun ta yi nazari.

Ya ce babu wani bayanan Gwamnati da ya nuna akwai wata makaranta mai suna Town Primary School kamar yadda Gobir ya ce ita ce makarantar da ya kammala kuma ta bashi satifiket.

Haka ma Akinboro ya bayyana cewar masu kara sun yi kokarin gamsar da kotu da hujjoji ta yadda shaidu 32 da suka kunshi jami’an Hukumar Zabe, Shugaban jam’iyyar PDP, shugaban makamai na Town Primary School Sabon-Birni da sauransu sun bayyana a gaban kotun sun kuma gabatar da takardu.

Ya ce a bisa ga hujjojin da suka gabatar, masu kariyar ba su cancanta da shiga zaben ba a bisa ga rashin takardu, don haka an yi kuskuren ba su kuri’u. A kan wannan ya bukaci kotun da ta yi watsi da kuri’un Ahmed Aliyu ta kuma tabbatar da Sa’idu Umar a matsayin wanda ya samu nasara a zaben Gwamna na 18 ga Maris 2023.

Shi kuwa lauyan APC, Hassan Liman SAN ya kalubalanci batun bambancin suna wanda ya ce ba ya hana dan takara shiga zabe don haka a cewarsa tsara sunan Gwamna Aliyu ba illa ba ce a takardunsa.

Lauyan ya bukaci kotun da ta yi watsi da karar tare da tabbatar da zaben Gwamna Ahmed Aliyu da Mataimakinsa Idris Gobir.

Kotu
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dimokuradiyyar Nijeriya A Shekara 27:Ba Yabo Ba Fallasa
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Next Post
Kasashen Dake Kewayen Tekun Pasifik Suna Da Ikon Neman Diyya Daga Gwamnatin Japan Kan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ruwa Cikin Teku

Kasashen Dake Kewayen Tekun Pasifik Suna Da Ikon Neman Diyya Daga Gwamnatin Japan Kan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ruwa Cikin Teku

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.