ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Za Ta Yanke Hukuncin Shari’ar Zaben Gwamnan Sakkwato A Satumba

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
Kotu

Kotun sauraren shari’ar zaben Gwamnan Jihar Sakkwato za ta yanke hukuncin shari’ar zaben a watan Satumba a shari’ar da Sa’idu Umar da Jam’iyyar PDP suka shigar na kalubalantar zaben Gwamna Ahmed Aliyu Sokoto na jam’iyyar APC.

Bayan saurare tare da karbar rubutattun hujjojin karshe daga dukkanin bangarori a ranar Asabar, tawagar alkalai uku a karkashin jagorancin Haruna Mshelia sun adana ranar yanke hukuncin wanda suka ce za a bayyana ranar a cikin watan Satumba.

  • Shugaban Burundi: Sin Tana Son Hada Kai Da Kasar Burundi
  • APC A Jihar Kano Za Ta Yi Taron Addu’a Don Neman Nasara A Kotu

Mai kara, Sa’idu Umar da jam’iyyar PDP suna kalubalantar zaben Gwamna Ahmed Aliyu da Mataimakinsa, Idris Muhammad Gobir na jam’iyyar APC a bisa ga rashin takardu da sabawa dokokin zabe a zaben Gwamna na 18 ga watan Maris.

ADVERTISEMENT

A zaman kotun, jagoran lauyoyin masu kara, Aare Olumuyiwa Akinboro SAN ya bukaci kotun da ta yi la’akari da hujjoji da shaidun da suka gabatar daga wakilan jam’iyya wadanda suka tabbatar da sabawa dokokin a zaben wanda aka gudanar cike da tashin hankali.

Akinboro ya ce musamman hujjojin da suka gabatar wadanda suka nuna bambace- bambance a tsakanin satifiket din makarantar sakandire ta Gwamna Aliyu da na jami’a wadanda sun bambanta da wadanda ya gabatar a Hukumar Zabe.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

Lauyan ya kuma bukaci kotun da ta yi la’akari da kundin rajistar makarantar Town Primary School, Sabon- Birni daga 1986 -1987 da kuma takarda daga makarantar.

Ya yi bayanin dukkanin makarantun da ke da rajsita a Karamar Hukumar Sabon-Birni daga Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da Hukumar Ilimi da sauran hujjojin da ya bukaci kotun ta yi nazari.

Ya ce babu wani bayanan Gwamnati da ya nuna akwai wata makaranta mai suna Town Primary School kamar yadda Gobir ya ce ita ce makarantar da ya kammala kuma ta bashi satifiket.

Haka ma Akinboro ya bayyana cewar masu kara sun yi kokarin gamsar da kotu da hujjoji ta yadda shaidu 32 da suka kunshi jami’an Hukumar Zabe, Shugaban jam’iyyar PDP, shugaban makamai na Town Primary School Sabon-Birni da sauransu sun bayyana a gaban kotun sun kuma gabatar da takardu.

Ya ce a bisa ga hujjojin da suka gabatar, masu kariyar ba su cancanta da shiga zaben ba a bisa ga rashin takardu, don haka an yi kuskuren ba su kuri’u. A kan wannan ya bukaci kotun da ta yi watsi da kuri’un Ahmed Aliyu ta kuma tabbatar da Sa’idu Umar a matsayin wanda ya samu nasara a zaben Gwamna na 18 ga Maris 2023.

Shi kuwa lauyan APC, Hassan Liman SAN ya kalubalanci batun bambancin suna wanda ya ce ba ya hana dan takara shiga zabe don haka a cewarsa tsara sunan Gwamna Aliyu ba illa ba ce a takardunsa.

Lauyan ya bukaci kotun da ta yi watsi da karar tare da tabbatar da zaben Gwamna Ahmed Aliyu da Mataimakinsa Idris Gobir.

Kotu
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Shekara 200 Bayan Shehu Ɗan Fodiyo: Hubbarensa Na Ci Gaba Zama Wajen Ziyara Da Neman Tabarruki
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Labarai

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
Labarai

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Next Post
Kasashen Dake Kewayen Tekun Pasifik Suna Da Ikon Neman Diyya Daga Gwamnatin Japan Kan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ruwa Cikin Teku

Kasashen Dake Kewayen Tekun Pasifik Suna Da Ikon Neman Diyya Daga Gwamnatin Japan Kan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ruwa Cikin Teku

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.