• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Birtaniya Ta Umarci Lauyan Ibori Ya Biya Tarar £28m

by Abubakar Abba
2 years ago
Birtaniya

Wata kotu a Birtaniya, ta umarci Bhadresh Gohil, lauyan tsohon gwamnan jihar Delta, James Ibori da ya biya tarar Fam miliyan 28 bisa taimaka wa da ya yi na boye kudaden da ya samu ta haramtacciyar hanya.

Gohil wanda dan kasar Indiya ne, kotun ta yanke masa hukuncin dauri a 2010 kan tukume-tuhume 13 na yin safarar kudade ta haramtacciyar hanya da da kuma aikata sauran laifukan da ke da nasaba da taimakawa Ibori na boye haramtattun kudade.

  • NLC Ta Bai Wa Tinubu Kwanaki 7 Don Dawo Da Tallafin Mai, Ko Ta Shiga Yajin Aiki 
  • Likitoci Masu Sanin Makamar Aiki Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-Ta-Gani

Ibori, ya shugabanci jihar Delta ne, daga shekarar 1999 zuwa shekarar 2007.

Kazalika, kotun a zamanta na jiya Litinin ta umarci Gohil da ya biya tarar sama da Fam miliyan 28, kuma zai kara fuskantar wani daurin na shekara shida.

Kafar yada labarai ta Reuters, a jiya Litinin ta kafa hujjarta ne da sanarwar da ta samu daga ofishin yanke hukunci na CPS na Birtaniya.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

Kotun dai, ta yanke Gohil hukuncin zaman gidan yari na shekaru 10 ne a 2010, wanda ya yi zaman rabin hukuncin, a gidan yari.

Kotun ta dauki wannan matakin ne, bayan ta yanke wa Ibori hukuncin dauri kan safarar haramtattun miliyoyin kudade a Birtaniya da wasu wuraren, inda kuma kotun a ranar Juma’ar da ta wuce, ta umarce shi da ya biya tarar Fam miliyan 101.5 wanda ya yi daidai da dala miliyan 130, ko kuma ya kara fuskantar wani hukuncin dauri na shekaru takwas.

Sai dai, a ranar Juma’ar, Ibori ya lashi takobin daukaka kara kan wannan hukunci, wanda aka yanke masa.

Bisa ga bayanan da kafar yada labarai ta Reuters samu daga ofishin CPS da ke a Birtaniya a karkashin dokar samun bayanai, bayan da Birtaniya ta karfafa dokar aikata manyan laifuka a shekarar 2002, laifin kwace kayan Ibori shi ne mafi girma na biyu, inda kuma na lauyansa Gohil ya kasance mafi girma na biyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100
Labarai

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi
Labarai

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Next Post
Jami’an Tsaro Sun Tsare Shugaban Nijar Kan Fargabar Yunkurin Juyin Mulki

Jami'an Tsaro Sun Tsare Shugaban Nijar Kan Fargabar Yunkurin Juyin Mulki

LABARAI MASU NASABA

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Birtaniya

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.