• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ku Yi Amfani Da Damar Da Arewa-maso-Yamma Ta Samu Na Karfafa Nasarar Ci Gaba – Fall

by Muhammad and Leadership Hausa
12 months ago
in Labarai
0
Ku Yi Amfani Da Damar Da Arewa-maso-Yamma Ta Samu Na Karfafa Nasarar Ci Gaba – Fall
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da Kungiyar Gwamnonin Arewa maso Yamma da Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya ke yunkurin tabbatar da dorewar zaman lafiya a yankin, babban jami’in kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya.

Mohamed Malick Fall, ya yi kira ga masu ruwa da tsaki da su yi amfani da damar da yankin Arewa-maso-Yamma ya samu masu yawa ta hanyar karfafa nasarar cimma muradun ci gaba mai dorewa (SDGs) da kuma kafa hanyar samar da ci gaba na dogon lokaci da magance matsalolin al’ummar yankin.

  • Babu Mai Faɗa Maka Matsalar Tsaro Daga Amurka Fiye Da Wanda Abin Ya Shafa – Radda
  • Tsaro: Gwamnoni Arewa Maso Yamma Za Su Yi Taro Domin Neman Mafita A Katsina

    “Bari mu kuma shiga cikin babbar damar da yankin ke da ita don karfafa nasarorin da aka samu na SDGs da kuma kafa hanyar samar da ci gaba mai dorewa a yankin. Mu zabi ba da fifiko wajen daidaita rarrabuwar kawuna da haduwar juna don bunkasa dabi’un hakuri da mutunta juna da sulhu da mutuncin dan Adam.”

Ya bayyana hakan ne a taron farko na zaman lafiya da tsaro na yankin Arewa maso Yamma da ke gudana a ranakun 24 zuwa 25 ga watan Yunin 2024, a Katsina.

Fall ya lura cewa, don magance kalubalen da ake fuskanta a yankin Arewa maso Yamma yadda ya kamata, zai bukaci hanyoyin da za a bi a fannoni daban-daban a fannin ayyukan jin kai, ci gaba da gina zaman lafiya, wannan, a cewarsa, “Zai ba mu damar karfafa matakan tsaro ta yadda za a magance matsalolin da suka addabe su kamar karancin albarkatun kasa, magance zurfafa rashin daidaiton tattalin arziki, da magance rarrabuwar kabilanci da addini wadanda dukkansu ke da tushe.”

Ko’odinetan ya jaddada cewa, ya kamata mu mai da hankali wajen inganta harkokin gudanar da mulki tare da tabbatar da adalci, ilimi, samar da walwala, inda ya ce ta hanyar inganta huldar da ke tsakanin gwamnati da ’yan qasa, ita ce babbar yarjejeniya ta zamantakewa. Za mu iya ganin waxannan tsare-tsaren suna canzawa ta hanya mai dorewa don ciyar da ajandar zaman lafiya a Nijeriya.

“A yau mun kuduri aniyar daukar matakan samar da zaman lafiya wanda zai ciyar da ajandar SDG gaba, da kuma gina Nijeriya wanda hakan zai bai wa kowa damar gudanar da ‘yancinsa da cikakken iko.
Majalisar Dinkin Duniya tana goyon bayan Nijeriya a kokarinmu na hadin gwiwa don tallafa wa daidaito, ‘yancin dan adam da wadata ga kowa da kowa,” a cewar Fall.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Taron mai taken “Haɗin Kai Tsakanin Yankuna Don Tabbatar Da Rayuwa Da Walwala A Yankin Arewa Maso Yammacin Nijeriya,” ya samu halartar Mataimakin Shugaban Kasar Tarayyar Nijeriya Sanata Kashim Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A jawabinsa na musamman, Shettima ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta qaddamar da shirin sake mayar da jama’ar Pulaku muhallinsu a matsayin wani shiri na kishin kasa domin magance wasu matsalolin da ke haifar da rigingimu da rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma.

“Za a fara aikin gwajin ne a Jihohin Sokoto, Kebbi, Benue, Katsina, Zamfara, Neja da Kaduna”. Shettima ya jaddada cewa, “Sakamakon shirin ya hada da gina gidaje, tituna, makarantu da muhimman ababen more rayuwa, wanda ke nuni da kudurin gwamnati na samar da ci gaba mai dorewa da kuma dunkulewar kasa, lumana da wadata Nijeriya.”

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa Maso Yamma kuma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya jaddada muhimmancin hadin kan yankin wajen magance matsalar rashin tsaro. Ya kuma bayyana kokarin kungiyar gwamnonin Arewa maso Yamma wajen magance matsalolin da suka hada da tsaro, noma, da samar da wutar lantarki.

Gwamna Radda ya bayyana cewa, “Gwamnonin sun kaddamar da wasu tsare-tsare na tsaro a jihohinsu, kamar kungiyar Community Watch Corps da ke Katsina, domin yin aiki tare da jami’an tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaArewaFallGwamnoniNijeriyaTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Alhaji Daga Zamfara Ya Mayar Da Maƙudan Kuɗaɗen Da Ya Tsinta A Makkah

Next Post

Peng Liyuan Da Uwargidan Shugaban Poland Sun Ziyarci Cibiyar Gabatar Da Wasannin Fasahohi Ta Sin

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

2 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

4 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

5 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

9 hours ago
Arewa
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

10 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

11 hours ago
Next Post
Peng Liyuan Da Uwargidan Shugaban Poland Sun Ziyarci Cibiyar Gabatar Da Wasannin Fasahohi Ta Sin

Peng Liyuan Da Uwargidan Shugaban Poland Sun Ziyarci Cibiyar Gabatar Da Wasannin Fasahohi Ta Sin

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.