ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ku Yi Amfani Da Damar Da Arewa-maso-Yamma Ta Samu Na Karfafa Nasarar Ci Gaba – Fall

by Muhammad and Leadership Hausa
2 years ago
Arewa

Yayin da Kungiyar Gwamnonin Arewa maso Yamma da Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya ke yunkurin tabbatar da dorewar zaman lafiya a yankin, babban jami’in kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya.

Mohamed Malick Fall, ya yi kira ga masu ruwa da tsaki da su yi amfani da damar da yankin Arewa-maso-Yamma ya samu masu yawa ta hanyar karfafa nasarar cimma muradun ci gaba mai dorewa (SDGs) da kuma kafa hanyar samar da ci gaba na dogon lokaci da magance matsalolin al’ummar yankin.

  • Babu Mai Faɗa Maka Matsalar Tsaro Daga Amurka Fiye Da Wanda Abin Ya Shafa – Radda
  • Tsaro: Gwamnoni Arewa Maso Yamma Za Su Yi Taro Domin Neman Mafita A Katsina

    “Bari mu kuma shiga cikin babbar damar da yankin ke da ita don karfafa nasarorin da aka samu na SDGs da kuma kafa hanyar samar da ci gaba mai dorewa a yankin. Mu zabi ba da fifiko wajen daidaita rarrabuwar kawuna da haduwar juna don bunkasa dabi’un hakuri da mutunta juna da sulhu da mutuncin dan Adam.”

Ya bayyana hakan ne a taron farko na zaman lafiya da tsaro na yankin Arewa maso Yamma da ke gudana a ranakun 24 zuwa 25 ga watan Yunin 2024, a Katsina.

Fall ya lura cewa, don magance kalubalen da ake fuskanta a yankin Arewa maso Yamma yadda ya kamata, zai bukaci hanyoyin da za a bi a fannoni daban-daban a fannin ayyukan jin kai, ci gaba da gina zaman lafiya, wannan, a cewarsa, “Zai ba mu damar karfafa matakan tsaro ta yadda za a magance matsalolin da suka addabe su kamar karancin albarkatun kasa, magance zurfafa rashin daidaiton tattalin arziki, da magance rarrabuwar kabilanci da addini wadanda dukkansu ke da tushe.”

ADVERTISEMENT

Ko’odinetan ya jaddada cewa, ya kamata mu mai da hankali wajen inganta harkokin gudanar da mulki tare da tabbatar da adalci, ilimi, samar da walwala, inda ya ce ta hanyar inganta huldar da ke tsakanin gwamnati da ’yan qasa, ita ce babbar yarjejeniya ta zamantakewa. Za mu iya ganin waxannan tsare-tsaren suna canzawa ta hanya mai dorewa don ciyar da ajandar zaman lafiya a Nijeriya.

“A yau mun kuduri aniyar daukar matakan samar da zaman lafiya wanda zai ciyar da ajandar SDG gaba, da kuma gina Nijeriya wanda hakan zai bai wa kowa damar gudanar da ‘yancinsa da cikakken iko.
Majalisar Dinkin Duniya tana goyon bayan Nijeriya a kokarinmu na hadin gwiwa don tallafa wa daidaito, ‘yancin dan adam da wadata ga kowa da kowa,” a cewar Fall.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Taron mai taken “Haɗin Kai Tsakanin Yankuna Don Tabbatar Da Rayuwa Da Walwala A Yankin Arewa Maso Yammacin Nijeriya,” ya samu halartar Mataimakin Shugaban Kasar Tarayyar Nijeriya Sanata Kashim Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A jawabinsa na musamman, Shettima ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta qaddamar da shirin sake mayar da jama’ar Pulaku muhallinsu a matsayin wani shiri na kishin kasa domin magance wasu matsalolin da ke haifar da rigingimu da rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma.

“Za a fara aikin gwajin ne a Jihohin Sokoto, Kebbi, Benue, Katsina, Zamfara, Neja da Kaduna”. Shettima ya jaddada cewa, “Sakamakon shirin ya hada da gina gidaje, tituna, makarantu da muhimman ababen more rayuwa, wanda ke nuni da kudurin gwamnati na samar da ci gaba mai dorewa da kuma dunkulewar kasa, lumana da wadata Nijeriya.”

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa Maso Yamma kuma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya jaddada muhimmancin hadin kan yankin wajen magance matsalar rashin tsaro. Ya kuma bayyana kokarin kungiyar gwamnonin Arewa maso Yamma wajen magance matsalolin da suka hada da tsaro, noma, da samar da wutar lantarki.

Gwamna Radda ya bayyana cewa, “Gwamnonin sun kaddamar da wasu tsare-tsare na tsaro a jihohinsu, kamar kungiyar Community Watch Corps da ke Katsina, domin yin aiki tare da jami’an tsaro.

Arewa
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa
Arewa
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Peng Liyuan Da Uwargidan Shugaban Poland Sun Ziyarci Cibiyar Gabatar Da Wasannin Fasahohi Ta Sin

Peng Liyuan Da Uwargidan Shugaban Poland Sun Ziyarci Cibiyar Gabatar Da Wasannin Fasahohi Ta Sin

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.