ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ku Yi Amfani Da Damar Da Arewa-maso-Yamma Ta Samu Na Karfafa Nasarar Ci Gaba – Fall

by Muhammad and Leadership Hausa
2 years ago
Arewa

Yayin da Kungiyar Gwamnonin Arewa maso Yamma da Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya ke yunkurin tabbatar da dorewar zaman lafiya a yankin, babban jami’in kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya.

Mohamed Malick Fall, ya yi kira ga masu ruwa da tsaki da su yi amfani da damar da yankin Arewa-maso-Yamma ya samu masu yawa ta hanyar karfafa nasarar cimma muradun ci gaba mai dorewa (SDGs) da kuma kafa hanyar samar da ci gaba na dogon lokaci da magance matsalolin al’ummar yankin.

  • Babu Mai Faɗa Maka Matsalar Tsaro Daga Amurka Fiye Da Wanda Abin Ya Shafa – Radda
  • Tsaro: Gwamnoni Arewa Maso Yamma Za Su Yi Taro Domin Neman Mafita A Katsina

    “Bari mu kuma shiga cikin babbar damar da yankin ke da ita don karfafa nasarorin da aka samu na SDGs da kuma kafa hanyar samar da ci gaba mai dorewa a yankin. Mu zabi ba da fifiko wajen daidaita rarrabuwar kawuna da haduwar juna don bunkasa dabi’un hakuri da mutunta juna da sulhu da mutuncin dan Adam.”

Ya bayyana hakan ne a taron farko na zaman lafiya da tsaro na yankin Arewa maso Yamma da ke gudana a ranakun 24 zuwa 25 ga watan Yunin 2024, a Katsina.

Fall ya lura cewa, don magance kalubalen da ake fuskanta a yankin Arewa maso Yamma yadda ya kamata, zai bukaci hanyoyin da za a bi a fannoni daban-daban a fannin ayyukan jin kai, ci gaba da gina zaman lafiya, wannan, a cewarsa, “Zai ba mu damar karfafa matakan tsaro ta yadda za a magance matsalolin da suka addabe su kamar karancin albarkatun kasa, magance zurfafa rashin daidaiton tattalin arziki, da magance rarrabuwar kabilanci da addini wadanda dukkansu ke da tushe.”

ADVERTISEMENT

Ko’odinetan ya jaddada cewa, ya kamata mu mai da hankali wajen inganta harkokin gudanar da mulki tare da tabbatar da adalci, ilimi, samar da walwala, inda ya ce ta hanyar inganta huldar da ke tsakanin gwamnati da ’yan qasa, ita ce babbar yarjejeniya ta zamantakewa. Za mu iya ganin waxannan tsare-tsaren suna canzawa ta hanya mai dorewa don ciyar da ajandar zaman lafiya a Nijeriya.

“A yau mun kuduri aniyar daukar matakan samar da zaman lafiya wanda zai ciyar da ajandar SDG gaba, da kuma gina Nijeriya wanda hakan zai bai wa kowa damar gudanar da ‘yancinsa da cikakken iko.
Majalisar Dinkin Duniya tana goyon bayan Nijeriya a kokarinmu na hadin gwiwa don tallafa wa daidaito, ‘yancin dan adam da wadata ga kowa da kowa,” a cewar Fall.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Taron mai taken “Haɗin Kai Tsakanin Yankuna Don Tabbatar Da Rayuwa Da Walwala A Yankin Arewa Maso Yammacin Nijeriya,” ya samu halartar Mataimakin Shugaban Kasar Tarayyar Nijeriya Sanata Kashim Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A jawabinsa na musamman, Shettima ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta qaddamar da shirin sake mayar da jama’ar Pulaku muhallinsu a matsayin wani shiri na kishin kasa domin magance wasu matsalolin da ke haifar da rigingimu da rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma.

“Za a fara aikin gwajin ne a Jihohin Sokoto, Kebbi, Benue, Katsina, Zamfara, Neja da Kaduna”. Shettima ya jaddada cewa, “Sakamakon shirin ya hada da gina gidaje, tituna, makarantu da muhimman ababen more rayuwa, wanda ke nuni da kudurin gwamnati na samar da ci gaba mai dorewa da kuma dunkulewar kasa, lumana da wadata Nijeriya.”

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa Maso Yamma kuma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya jaddada muhimmancin hadin kan yankin wajen magance matsalar rashin tsaro. Ya kuma bayyana kokarin kungiyar gwamnonin Arewa maso Yamma wajen magance matsalolin da suka hada da tsaro, noma, da samar da wutar lantarki.

Gwamna Radda ya bayyana cewa, “Gwamnonin sun kaddamar da wasu tsare-tsare na tsaro a jihohinsu, kamar kungiyar Community Watch Corps da ke Katsina, domin yin aiki tare da jami’an tsaro.

Arewa
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje
Arewa
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Peng Liyuan Da Uwargidan Shugaban Poland Sun Ziyarci Cibiyar Gabatar Da Wasannin Fasahohi Ta Sin

Peng Liyuan Da Uwargidan Shugaban Poland Sun Ziyarci Cibiyar Gabatar Da Wasannin Fasahohi Ta Sin

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.