• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kudaden ‘Yan Majalisa: Wa Za A Gaskata Tsakanin Hukumar Albashi Da Kawu Sumaila?

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Labarai
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Batun yawan makudan kudaden da ‘yan majalisar tarayya ke karba na ci gaba da tayar da kura a Nijeriya bisa yadda aka samu bayanai masu cin karo da juna a tsakanin Hukumar Rabon Albashi ta Kasa (RMAFC) da kuma wani Sanata mai ci daga Jihar Kano, Abdurrahman Kawu Sumaila.

 

Ita dai hukumar, ta bayyana cewa kowane dan majalisar dattawa yana amsar albashi da alawus a kowani kimanin Naira 1,063,860, yayin da shi kuma Sanatan ya bayyana cewa Naira miliyan 21 ake biyan su a matsayin kudin gudanarwa.

  • Shirin 3MTT Zai Samar Wa Matasa Miliyan Uku Aikin Yi, inji Ministan Yaɗa Labarai
  • Mutum 3 Sun Rasa Rayukansu Yayin Da Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Ƙauyuka A Bauchi

Hukumar ta ce daga cikin dunkulallen albashin da ake biyansu da alawus, akwai tsurar albashin Naira 168,866:70, sai alawus din mai da kula da motocin naira 126,650 da naira 42,216:66, mataimaka da ma’aikatan gida naira 126,650:00, nishadi naira 50,660:00, kayayyakin aiki naira 50,660, kudin sayen jaridu naira 25,330:00, alawus din tufafi naira 42,216,66:00, kula da gida naira 8,443.33 da kuma alawus na mazabu naira 422,166:66.

 

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Shugaban RMAFC, Muhammed Bello Shehu ne ya bayyana hakan a ranar Talata a martanin da yake mayarwa kan cece-kucen da ake yi dangane da ainihin albashi da alawus-alawus da ake biyan ‘yan majalisar dokokin tarayyar Nijeriya.

 

Sai dai shugaban hukumar wanda doka ta ba ta ikon daidaita albashi da alawus-alawus na masu rike da mukaman siyasa, ya ce wasu alawus-alawus ne na yau da kullum ne, yayin da wasu kuma ba na yau da kullum ba ne. A cewarsa, ana biyan alawus-alawus na yau da kullum tare da albashi, yayin da ake biyan alawus na musamman daban. Misali, akwai alawus na kayan daki naira miliyan 6,079,200 da garaturi da ake biya sau daya a kowane wa’adin mulki, sai kuma alawus din motoci na naira miliyan 8,105,600, wanda shi rance ne da za a biya bayan dan majalisa ya bar ofishi.

 

“Idan aka yi la’akari da albashin sanatoci na wata-wata, za a ga cewa kowane sanata na karbar albashi da alawus-alawus na naira 1,063,860:00 a duk wata, wanda ya kunshi gundarin albashi nai naira 168,866:70 da kudin man motoci na naira 126, 650:00 da kudin mataimaka na naira 42,216:66 da ma’aikata nai naira 216,66:00 da kula da gida naira 8,443.33:00 da kuma alawus na mazabu na naira 422,166:66,” kamar yadda Shugaban RMAFC ya bayyana a wata sanarwa da ya sanya wa hannu a ranar Talata.

 

Ya kuma jaddada cewa in ban da wasu tsirarun masu rike da mukaman siyasa da na gwamnati irinsu shugaban kasa, mataimakin shugaban kasa, shugaban majalisar dattawa, shugaban majalisar wakilai da sauran su, duk jami’an gwamnati da na majalisa ba a ba su gidaje kamar yadda aka saba a lokutan baya.
“Hukumar kuma tana son yin amfani da wannan dama wajen bayyana cewa duk wani zargi da ake yi game da wasu alawus-alawus da masu rike da mukamin siyasa, ko ma’aikacin gwamnati ke dauka a wajen da aka tanadar a cikin dokar albashi ta shekarar 2008, ya kamata a yi bayaninsa daga wanda ya yi zargin.

 

“Don kauce wa yada bayanan da ba su dace ba da kuma bata suna da ake yaudarar ‘yan kasa da sauran mutanen duniya, hukumar ta ga ya fi dacewa ta sanar wa ‘yan Nijeriya da duk wani mai sha’awar samun cikakkun bayanai da suka kunshi albashin masu rike da mukaman siyasa, da jami’an gwamnati, ya garzaya adireshin intanet na hukumar: www.rmafc.gob.ng, zai ga komai dalla-dalla” in ji shi.

 

Haka nan ya kara da cewa, tsarin mulkin kasa bai wa Hukumar RMAFC ikon tilasta aiki da abin da ta tsara a matsayin albashi ba, inda ya ce majalisar dokoki ta kasa ce ke da hurumin yin hakan.

Sai dai kuma, Sanata Kawu Sumaila na jam’iyyar hamayya ta NNPP ya ce kudaden gudanarwar da yake samu a matsayinsa na dan majalisar dattawa da ya kunshi har da tafiyar da ofishinsa ya kai naira miliyan 21 a kowane wata.

 

Kawu Sumaila wanda ya ce miliyoyin ba wasu kudade ba ne masu yawa da ‘yan majalisar ke samu da har za su zama wani abin cece-kuce, ya bayyana hakan ne ga BBC Hausa, bayan shugaban hukumar ta rabon albashi ya yi wadancan bayanan na sama.

 

“Kudin da ake karba na albashi a wata bai kai naira miliyan daya ba, idan an yi yanke-yanke yakan dawo kamar naira dubu dari shida da dan wani abu a matsayin albashi,” in ji sanatan.

 

Ya ce hukumar tattara kudaden shiga da raba su ta Nijeriya ce ta yanka wa ‘yan majalisar albashin.
“Saboda kari da aka samu, a majalisar dattawa ana ba wa kowane sanata naira miliyan ashirin da daya a kowane wata a matsayin kudin gudanar da ofishinsa,” in ji shi.

 

Ya kara da cewa jimillar naira miliyan 22 yake samu a matsayinsa na sanata.
Ya ce kudaden da yake karba su ne na dukkanin ayyukan da zai yi da suka hada da tafiye-tafiyen dan majalisa na cikin gida da sayen jaridu.

 

Ya ce bai san adadin kudin da shugabannin majalisar ke karba ba a matsayin albashi da na gudanarwa.
Sanatan ya caccaki Obasanjo, inda ya ce a zamanin mulkinsa ne aka fara ba ‘yan majalisa kudaden da suke wuce hankalin mutane da nufin gyara ga kundin tsarin mulki domin sahale masa yin tazarce, zargin da a baya tsohon shugaban ya musanta.

 

Idan za a tuna, a kwanakin baya ne tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo ya yi zargin cewa ‘yan majalisar tarayya suna biyan kansu albashi da alawus-alawus na wata-wata wanda ya saba wa dokoki. Haka kuma, tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani, ya taba bayyana cewa kowane sanata na karbar kudin gudanar da aiki a kowane wata na naira miliyan 13.5, baya ga karin naira 750,000 da hukumar ta tsara duk wata.

 

Wannan cacar baki na zuwa a daidai lokacin da ake fama da tsadar rayuwa a Nijeriya.
Wasu ‘yan Nijeriya na ganin makudan kudaden da ake biyan ‘yan majalisar na daga cikin dalilan da ke jefa su cikin kunci, yayin da su kuma ‘yan majalisar ke ganin nasu kawai ake gani, amma ba a dub ana bangaren zartarwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Amince Da Karin Albashi Da Kashi 300 Ga Alkalan Nijeriya

Next Post

Girman Manzon Allah (SAW): Darasi Daga Suratul Fat’hi (I)

Related

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

1 hour ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

2 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

3 hours ago
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

4 hours ago
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
Labarai

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

6 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

8 hours ago
Next Post
Manzon Allah

Girman Manzon Allah (SAW): Darasi Daga Suratul Fat’hi (I)

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.