• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kujerar Ɗindindin A Majalisar Dinkin Duniya: Tinubu Na Kamun Ƙafa Wurin Shugabannin G20

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Kujerar Ɗindindin A Majalisar Dinkin Duniya: Tinubu Na Kamun Ƙafa Wurin Shugabannin G20
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu ya ce akwai bukatar kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya yi garambawul a tsarinsa domin tabbatar da ci gaba da dacewarsa a harkokin duniya.

Shugaban, wanda ya nanata shirye-shiryen da NIjeriya ke da ita na wakiltar Afirka a cikin Majalisar Dinkin Duniya, ya yi kira ga shugabannin kungiyar G20 da su amince Nahiyar Afirka ta samu kujeran dindindin a Majalisar Dinkin Duniya.

  • Tsarabar Taron Kolin G20
  • Jami’in Yada Labarai: Kasar Sin A Shirye Take Ta Aiwatar Da Hadin Gwiwar Kasashe Na Hakika Tare Da Mambobin G20

Ya yi wannan rokon ne a taron koli na shugabannin kungiyar G20 karo na 19 a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil.

Shugaba Tinubu ya ce, “Ya kamata kwamitin tsaro ya fadada rukunin mambobi na dindindin da wadanda ba na dindindin ba don nuna bambance-bambancen duniya da yawan jama’a, domin Afirka ta cancanci a ba ta kujeran dindindin a Majalisar Dinkin Duniya.

“Afirka ta cancanci fifiko a wannan tsari, kuma ya kamata a ba ta kujeru biyu na dindindin tare da daidaita matsayinta. A sherye Nijeriya take ta zama wakiliyar Afirka a wannan matsayi.”

Labarai Masu Nasaba

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Sanarwar ta shugaban wadda Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar ya karanta a madadinsa, ta yi nuni da cewa, kungiyar G20 a halin yanzu tana sanye da wani tsari na cibiyoyi na kasa da kasa masu sa ido da ke goyon bayan ra’ayin sauye-sauye a bangarori da yawa.

Ya kuma yaba wa matakin da G20 ta dauka na bai wa kungiyar tarayyar Afirka damar zama mamba ta dindindin da kuma yadda take gayyatar kasashen da za su shiga kungiyar.

Shugaba Tinubu ya kuma yaba da kafa kungiyar kawance na yaki da yunwa da kuma fatara, wanda Shugaban kasar Brazil, Luiz Lula da Silba ke jagoranta, yana mai cewa kawancen na da matukar muhimmanci wajen yaki da yunwa da fatara a duniya.

Sannan ya yaba da shirin tare da bayyana shi a matsayin matakin da ya dace don magance daya daga cikin manyan kalubalen duniya.

Shugaba Tinubu ya kwatanta wannan shiri na duniya da daya daga cikin fannoni takwas da ya zayyana a bikin rantsar da shi watanni 18 da suka gabata, inda ya bayyana aniyar Nijeriya na daukar kyawawan halaye na kasa da kasa don ciyar da tattalin arzikinta gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: G20
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dokar Haraji Ta Gwamnatin Tinubu Za Ta Illata Arewa

Next Post

Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (2)

Related

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

58 minutes ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

3 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

5 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

7 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

7 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

8 hours ago
Next Post
Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (2)

Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (2)

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.