• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Chelsea Ta Girmama Ni – Thomas Tuchel

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Kungiyar Chelsea Ta Girmama Ni – Thomas Tuchel
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon kociyan kungiyar kwallon kafa ta Chelsea, Thomas Tuchel ya ce an ”martaba shi” da ya samu damar bayar da gudunmuwa a kungiyar, kuma ba zai manta rawar da ya taka a kungiyar ba har abada.

A satin da ya gabata ne Chelsea ta kori Tuchel, mai shekara 49, bayan da ya ja ragamar kungiyar wasanni sama da 100, bayan da ya yi rashin nasara a gidan kungiyar Dinamo Zagreb a gasar cin kofin zakarun turai da ci 1-0 a wasan farko na cikin rukuni.

  • Chelsea Ta Nada Potter A Matsayin Sabon Kocinta

Chelsea ta nada kociyan kungiyar Brighton Hobe Albion, Graham Potter, domin ya ci gaba da horar da kungiyar, wanda ya amince da fam miliyan 21 tare da tawagarsa ta masu taimaka masa.
Mai koyarwa Tuchel ya ce ya ”kadu” da jin labarin cewa an kore shi daga aikinsa sannan tsohon kociyan na Borussia Dortmund da Paris St-Germain ya bar Stamford Bridge, bayan ya lashe kofuna uku a watanni 20 da ya ja ragamar kungiyar inda ya lashe gasar cin kofin zakarun turai na Champions League a kakar wasa ta 2020 zuwa 2021 a kakar farko da ya ja ragamar Chelsea.

Chelsea wadda ta sanar da korar Tuchel ta kara da cewar, sabon wanda ya mallaki kungiyar, Todd Bohley ya gamsu cewar ta sallami kocin a lokacin da ya dace domin yana fatan gina sabuwar Chelsea.

”Wannan kungiya ce da nake jin tamkar gida ce a waje na ina godiya ga dukkan wadanda suka taimaka min gudanar da aiki da ‘yan wasa da magoya baya, wadanda kullum suke min tarbar girma tun daga ranar farko” In ji Tuchel.

Labarai Masu Nasaba

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Ya kara da cewa ”Farin ciki na da alfaharin da na taimaka kungiyar ta lashe Champions League da kuma Club World Cup ba zai taba gushewa ba a rayuwata domin martaba ce da na samu damar bayar da gudunmuwa a kungiyar, ba zan manta da sama da watanni 19 da na yi aiki a kungiyar ba, zan ci gaba da tunawa a rayuwata.

Chelsea tana ta shida a teburin gasar Premier League, bayan cin wasanni uku da canjaras daya da shan kashi a wasa daya kuma sabon wanda ya sayi Chelsea ya kashe fam miliyan £255, wajen sayo sababbin ‘yan wasa, kungiyar ta kafa tarihin kashe kudi a kaka daya wajen cefane.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Usman Bala

Next Post

Wani Dan China Ya Kashe Masoyiyarsa Da Wuka A Kano

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Wasanni

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

12 hours ago
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
Wasanni

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

15 hours ago
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

3 days ago
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
Wasanni

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

4 days ago
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
Wasanni

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

5 days ago
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
Wasanni

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

6 days ago
Next Post
Wani Dan China Ya Kashe Masoyiyarsa Da Wuka A Kano

Wani Dan China Ya Kashe Masoyiyarsa Da Wuka A Kano

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.