• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Chelsea Ta Girmama Ni – Thomas Tuchel

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Chelsea

Tsohon kociyan kungiyar kwallon kafa ta Chelsea, Thomas Tuchel ya ce an ”martaba shi” da ya samu damar bayar da gudunmuwa a kungiyar, kuma ba zai manta rawar da ya taka a kungiyar ba har abada.

A satin da ya gabata ne Chelsea ta kori Tuchel, mai shekara 49, bayan da ya ja ragamar kungiyar wasanni sama da 100, bayan da ya yi rashin nasara a gidan kungiyar Dinamo Zagreb a gasar cin kofin zakarun turai da ci 1-0 a wasan farko na cikin rukuni.

  • Chelsea Ta Nada Potter A Matsayin Sabon Kocinta

Chelsea ta nada kociyan kungiyar Brighton Hobe Albion, Graham Potter, domin ya ci gaba da horar da kungiyar, wanda ya amince da fam miliyan 21 tare da tawagarsa ta masu taimaka masa.
Mai koyarwa Tuchel ya ce ya ”kadu” da jin labarin cewa an kore shi daga aikinsa sannan tsohon kociyan na Borussia Dortmund da Paris St-Germain ya bar Stamford Bridge, bayan ya lashe kofuna uku a watanni 20 da ya ja ragamar kungiyar inda ya lashe gasar cin kofin zakarun turai na Champions League a kakar wasa ta 2020 zuwa 2021 a kakar farko da ya ja ragamar Chelsea.

Chelsea wadda ta sanar da korar Tuchel ta kara da cewar, sabon wanda ya mallaki kungiyar, Todd Bohley ya gamsu cewar ta sallami kocin a lokacin da ya dace domin yana fatan gina sabuwar Chelsea.

”Wannan kungiya ce da nake jin tamkar gida ce a waje na ina godiya ga dukkan wadanda suka taimaka min gudanar da aiki da ‘yan wasa da magoya baya, wadanda kullum suke min tarbar girma tun daga ranar farko” In ji Tuchel.

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Ya kara da cewa ”Farin ciki na da alfaharin da na taimaka kungiyar ta lashe Champions League da kuma Club World Cup ba zai taba gushewa ba a rayuwata domin martaba ce da na samu damar bayar da gudunmuwa a kungiyar, ba zan manta da sama da watanni 19 da na yi aiki a kungiyar ba, zan ci gaba da tunawa a rayuwata.

Chelsea tana ta shida a teburin gasar Premier League, bayan cin wasanni uku da canjaras daya da shan kashi a wasa daya kuma sabon wanda ya sayi Chelsea ya kashe fam miliyan £255, wajen sayo sababbin ‘yan wasa, kungiyar ta kafa tarihin kashe kudi a kaka daya wajen cefane.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0
Wasanni

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Next Post
Wani Dan China Ya Kashe Masoyiyarsa Da Wuka A Kano

Wani Dan China Ya Kashe Masoyiyarsa Da Wuka A Kano

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.