• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Chelsea Ta Girmama Ni – Thomas Tuchel

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Kungiyar Chelsea Ta Girmama Ni – Thomas Tuchel
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon kociyan kungiyar kwallon kafa ta Chelsea, Thomas Tuchel ya ce an ”martaba shi” da ya samu damar bayar da gudunmuwa a kungiyar, kuma ba zai manta rawar da ya taka a kungiyar ba har abada.

A satin da ya gabata ne Chelsea ta kori Tuchel, mai shekara 49, bayan da ya ja ragamar kungiyar wasanni sama da 100, bayan da ya yi rashin nasara a gidan kungiyar Dinamo Zagreb a gasar cin kofin zakarun turai da ci 1-0 a wasan farko na cikin rukuni.

  • Chelsea Ta Nada Potter A Matsayin Sabon Kocinta

Chelsea ta nada kociyan kungiyar Brighton Hobe Albion, Graham Potter, domin ya ci gaba da horar da kungiyar, wanda ya amince da fam miliyan 21 tare da tawagarsa ta masu taimaka masa.
Mai koyarwa Tuchel ya ce ya ”kadu” da jin labarin cewa an kore shi daga aikinsa sannan tsohon kociyan na Borussia Dortmund da Paris St-Germain ya bar Stamford Bridge, bayan ya lashe kofuna uku a watanni 20 da ya ja ragamar kungiyar inda ya lashe gasar cin kofin zakarun turai na Champions League a kakar wasa ta 2020 zuwa 2021 a kakar farko da ya ja ragamar Chelsea.

Chelsea wadda ta sanar da korar Tuchel ta kara da cewar, sabon wanda ya mallaki kungiyar, Todd Bohley ya gamsu cewar ta sallami kocin a lokacin da ya dace domin yana fatan gina sabuwar Chelsea.

”Wannan kungiya ce da nake jin tamkar gida ce a waje na ina godiya ga dukkan wadanda suka taimaka min gudanar da aiki da ‘yan wasa da magoya baya, wadanda kullum suke min tarbar girma tun daga ranar farko” In ji Tuchel.

Labarai Masu Nasaba

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

Ya kara da cewa ”Farin ciki na da alfaharin da na taimaka kungiyar ta lashe Champions League da kuma Club World Cup ba zai taba gushewa ba a rayuwata domin martaba ce da na samu damar bayar da gudunmuwa a kungiyar, ba zan manta da sama da watanni 19 da na yi aiki a kungiyar ba, zan ci gaba da tunawa a rayuwata.

Chelsea tana ta shida a teburin gasar Premier League, bayan cin wasanni uku da canjaras daya da shan kashi a wasa daya kuma sabon wanda ya sayi Chelsea ya kashe fam miliyan £255, wajen sayo sababbin ‘yan wasa, kungiyar ta kafa tarihin kashe kudi a kaka daya wajen cefane.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Usman Bala

Next Post

Wani Dan China Ya Kashe Masoyiyarsa Da Wuka A Kano

Related

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo
Wasanni

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

24 hours ago
Lookman
Wasanni

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

2 days ago
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG
Wasanni

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

4 days ago
Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya
Wasanni

Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya

4 days ago
Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana
Wasanni

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

5 days ago
‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana
Wasanni

‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana

5 days ago
Next Post
Wani Dan China Ya Kashe Masoyiyarsa Da Wuka A Kano

Wani Dan China Ya Kashe Masoyiyarsa Da Wuka A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

September 5, 2025
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

September 5, 2025
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

September 5, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

September 5, 2025
'Yan Bindiga

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

September 5, 2025
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

September 5, 2025
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.