• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Chelsea Ta Girmama Ni – Thomas Tuchel

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Kungiyar Chelsea Ta Girmama Ni – Thomas Tuchel
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon kociyan kungiyar kwallon kafa ta Chelsea, Thomas Tuchel ya ce an ”martaba shi” da ya samu damar bayar da gudunmuwa a kungiyar, kuma ba zai manta rawar da ya taka a kungiyar ba har abada.

A satin da ya gabata ne Chelsea ta kori Tuchel, mai shekara 49, bayan da ya ja ragamar kungiyar wasanni sama da 100, bayan da ya yi rashin nasara a gidan kungiyar Dinamo Zagreb a gasar cin kofin zakarun turai da ci 1-0 a wasan farko na cikin rukuni.

  • Chelsea Ta Nada Potter A Matsayin Sabon Kocinta

Chelsea ta nada kociyan kungiyar Brighton Hobe Albion, Graham Potter, domin ya ci gaba da horar da kungiyar, wanda ya amince da fam miliyan 21 tare da tawagarsa ta masu taimaka masa.
Mai koyarwa Tuchel ya ce ya ”kadu” da jin labarin cewa an kore shi daga aikinsa sannan tsohon kociyan na Borussia Dortmund da Paris St-Germain ya bar Stamford Bridge, bayan ya lashe kofuna uku a watanni 20 da ya ja ragamar kungiyar inda ya lashe gasar cin kofin zakarun turai na Champions League a kakar wasa ta 2020 zuwa 2021 a kakar farko da ya ja ragamar Chelsea.

Chelsea wadda ta sanar da korar Tuchel ta kara da cewar, sabon wanda ya mallaki kungiyar, Todd Bohley ya gamsu cewar ta sallami kocin a lokacin da ya dace domin yana fatan gina sabuwar Chelsea.

”Wannan kungiya ce da nake jin tamkar gida ce a waje na ina godiya ga dukkan wadanda suka taimaka min gudanar da aiki da ‘yan wasa da magoya baya, wadanda kullum suke min tarbar girma tun daga ranar farko” In ji Tuchel.

Labarai Masu Nasaba

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

Ya kara da cewa ”Farin ciki na da alfaharin da na taimaka kungiyar ta lashe Champions League da kuma Club World Cup ba zai taba gushewa ba a rayuwata domin martaba ce da na samu damar bayar da gudunmuwa a kungiyar, ba zan manta da sama da watanni 19 da na yi aiki a kungiyar ba, zan ci gaba da tunawa a rayuwata.

Chelsea tana ta shida a teburin gasar Premier League, bayan cin wasanni uku da canjaras daya da shan kashi a wasa daya kuma sabon wanda ya sayi Chelsea ya kashe fam miliyan £255, wajen sayo sababbin ‘yan wasa, kungiyar ta kafa tarihin kashe kudi a kaka daya wajen cefane.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Usman Bala

Next Post

Wani Dan China Ya Kashe Masoyiyarsa Da Wuka A Kano

Related

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu
Wasanni

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

9 hours ago
Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

17 hours ago
Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea
Wasanni

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

2 days ago
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata
Wasanni

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

3 days ago
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari
Wasanni

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

4 days ago
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa
Wasanni

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

5 days ago
Next Post
Wani Dan China Ya Kashe Masoyiyarsa Da Wuka A Kano

Wani Dan China Ya Kashe Masoyiyarsa Da Wuka A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.