ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa 5 Da Jam’iyyatu Ansariddeen Attijjaniyya Ta Nemi Gwamnati Ta Yi Kan Kan Kisan ‘Yan Maulidi A Kaduna 

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
kisa

Kungiyar Jam’iyyatu Ansariddeen Attijjaniyya ta lissafa wasu abubuwa guda biyar da take neman gwamnatin tarayya ta aiwatar bisa kisan kiyashi da jirgin sojojin Nijeriya ya yi wa masu bikin maulidi a kauyen Tudun Biri da ke Jihar Kaduna.

Kungiyar ta bayyana abubuwan ne a wani taron ‘yan jarida da ta kira a shalkwatarta da ke Abuja.

  • Sheikh Dahiru Bauchi Ya Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Masu Maulidi A Kaduna
  • Kotu Ta Yi Wa Mutane 4 Daurin Rai Da Rai Bisa Samun Su Da Laifin Daukar Nauyin Boko Haram

Cikina abubuwan da kungiyar ta nemi gwamnatin tarayya ta yi sun hada da gudanar da cikakken bincike cikin gaggawa kan tare da sabunta bayanai ga al’umma, saboda tabbatar da adalci.

ADVERTISEMENT

Haka kuma kungiyar ta ce dole ne a karfafa ka’idojin aiki a tsakanin sojojin Nijeriya, musamman ma na tura jiragen marasa matuKi.

Har ila yau, kungiyar ta bukaci a horar da sojoji sanin ‘yancin Dan’adam da kuma kare rayukan fararen hula tare da jaddada tausayawa da mutunta bambance-bambance da kuma fahimtar al’adu, wanda hakan na iya taimakawa wajen hana sake afkuwan wannan lamari.

LABARAI MASU NASABA

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Ta kuma yi kira da a samar da hadin kan a tsakanin sojoji da kuma al’umma.

Daga karshe, kungiyar ta nemi gwamnatin tartayya ta biya diyyar rayukan da aka salwantar ga iyalan wadanda lamarin ya shafa. Ta ce dole ne a tallafa wa rayuwar iyalan da suka rasa ‘yan’uwansu da kudade, domin sake rayuwarsu.

Da yake karin bayani, Babban Sakataren Kungiyar na Kasa, Alhaji Alkasim Yahaya ya bayyana cewa, “Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu a wannan mummunan lamari. Babu wata magana da za ta iya rage radadin da suke ciki, amma za mu ci gaba da yin addu’o’i a gare ku.

“Muna bakin cikin yadda wannan musiba ta faru a daidai lokacin da al’umma ke bikin murnar zagayowar haihuwar Annabi Muhammadu (SAW) cikin lumana. Muna kira da rundunar sojin Nijeriya ta gudanar da sahihin bincike kan lamari tare da daukan mataki ga duk wadanda aka samu da hannnu a ciki.

“A matsayinmu na kungiya, muna bukata a nuna gaskiya da rikon amana wajen hukunta wadanda suka aikata wannan kisan kiyashi. Mun san cewa babu wanda ya fi karfin doka, dole ne a hukunta wadanda suka aikata wannan ta’asa ga mabiyanmu ba tare da la’akari da matsayinsu ba,” in ji shi.

Kungiyar ta ce aikata wannan mummunan lamari ba karamin laifi ba ne na take hakkin Dan’adam, musamman a lokacin bikin zagayowar haihuwar Annabi (SAW) da masoya ‘yan Tijjaniyya ke yi duk shekara. Sannan kuma ta yi kira da rundunar sojin Nijeriya da gwamnatin tarayya da su gaggauta daukar mataki cikin gaggawa tare yin amfani da wadannan sharudda.

Ta ce a shirye take ta ba da goyon baya da hadin kai ga masu ruwa da tsaki domin kawo sauyi mai ma’ana da kwanciyar hankali a Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani
Labarai

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN
Manyan Labarai

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Next Post
Taron COP28: Ba Sharholiya Ce Ta Kai Tinubu Da Tawagarsa Dubai ba – Ministan Yada Labarai 

Taron COP28: Ba Sharholiya Ce Ta Kai Tinubu Da Tawagarsa Dubai ba - Ministan Yada Labarai 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

November 14, 2025
Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.