ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron COP28: Ba Sharholiya Ce Ta Kai Tinubu Da Tawagarsa Dubai ba – Ministan Yada Labarai 

by Sulaiman
3 years ago
COP28

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ba yawon sharholiya ce ta kai Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ‘yan tawagarsa a taron Majalisar Ɗinkin Duniya kan sauyin yanayi da ake yi a Dubai ba, kowa da aikin da zai yi a yayin taron.

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris ne ya bayyana hakan acikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai inda ya yi raddi kan masu zargin gwamnatin tarayya da fita da mutane fiye da kima zuwa taron na COP28 da ya gudana a kasar Dubai.

  • Sin Ta Sake Zama Memba A Rukunin A A Kungiyar IMO
  • Kasar Sin: Yawan Kunshin Kayayyaki Da Aka Isar A Kasar Ya Kafa Wani Sabon Tarihi

Idris ya ce gwamnati ta lura da maganganun da ake yi kan adadin ‘yan tawagar da su ka je Dubai domin halartar taron, kuma ta ga “akwai buƙatar ta samar da ƙarin haske kamar yadda ta yi alƙawarin za ta riƙa gudanar da al’amuran ta a bayyane tare da kasancewa mai fayyace komai ga jama’a dangane da abin da ya ke bukatar karin haske”

ADVERTISEMENT

A cewarsa, “Taron Masu Ruwa da Tsaki (Convention of Parties, COP) na Tsarin Shirye-shiryen Majalisar Ɗinkin Duniya kan Sauyin Yanayi, ‘UNFCCC’ shi ne mashahurin Taron Duniya kan Sauyin Yanayi wanda a bana ya samu halartar fiye da mutane 70,000 daga kasashe fiye da 100. Wakilcin da Nijeriya ta samu ya yi daidai da matsayinta na jagora mai faɗa a ji a Nahiyar Afirka kuma babbar mai taka rawa kan al’amarin sauyin yanayi, wato ‘climate action’.”

Ya ce waɗanda su ka halarci taron daga Nijeriya sun haɗa da jami’an gwamnati, wakilan ‘yan kasuwa da na ƙungiyoyi masu zaman kansu, da ‘yan sa kai, gwamnatocin jihohi, ‘yan jarida, hukumomin ƙasa da ƙasa, wakilan al’ummomin da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Idris ya bada lissafin ‘yan tawagar da su ka je a aljihun gwamnati su mutum 422, kamar haka:

idris ya bayyana cewa, Mutane 422 ne kacal suka halarci taron acikin aljihun gwamnati. Wadanda suka hada da Hukumar Sauyin Yanayi ta Ƙasa, 32; Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya, 34; Dukkan Ma’aikatu, 167; Fadar Shugaban Ƙasa, 67; Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, 9; Majalisar Tarayya, 40 sai kuma Hukumomin gwamnati da cibiyoyi, 73.

 

Ya bada tabbacin cewa a matsayin Nijeriya na wadda ta ke da ƙarfin tattalin arziki fiye da sauran ƙasashen Afrika kuma mafi yawan jama’a a nahiyar, kuma ta na da tattalin arziki da ake samu daga ma’adinai, wadda ke fuskantar barazanar sauyawar yanayi, ta na da muhimmin matsayi a batun sauyin yanayi, “don haka rawar da za mu taka a taron CCOP28 ba kaɗan ba ce.”

Ministan ya ƙara da cewa: “Taron COP28 ya bada damarmaki na zuba jari da ƙulla yarjejeniyoyin haɗin gwiwa a sassa daban-daban da sauyin yanayi ya shafe su, kuma yanzu haka Nijeriya ta fara cin moriyar shiga taron da ta yi, kamar yadda waɗannan al’amurran su ka shaida:

“Nijeriya da Jamus sun rattaba hannu kan gaggauta aiwatar da Shirin Shugaban Ƙasa kan Wutar Lantarki (PPI) domin inganta samar da lantarki a Nijeriya.

“Shugaba Tinubu ya jagoranci wani babban taro wanda masu ruwa da tsaki da masu zuba jari su ka yi kan Kasuwar Man Fetur ta Nijeriya da Shirin Kawo Motocin Sufuri masu aiki da hasken Rana a lokacin da ake taron ƙoli na COP28 kan sauyin yanayi.

“Akwai alamun Nijeriya za ta ci moriyar Asusun Asara Da Ɓarna (Loss and Damage Fund) wanda aka kafa a lokacin taron COP27 da aka yi a Masar kuma aka ƙaddamar da shi a wajen buɗe wannan taron na COP28 a Dubai. Asusun zai samar da kuɗaɗen da ba bashi ba ne waɗanda za a kashe don tallafa wa ƙasashen da tasirin sauyin yanayi ya fi shafarsu.

“Haka kuma, Shugaban Ƙasa ya yi taro da Shugaban Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) don tabbatar da yarjejeniyoyin da ke akwai a tsakanin ƙasashen biyu. Duk wannan ban da fa tattaunawar diflomasiyya da aka yi da ƙasashe da ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa daban-daban.”

“Ya kamata a sani cewa, a tsawon shekaru, Nijeriya ta tabbatar da matsayin ta kan batun sauyin yanayi ta hanyar zama ƙasar Afrika ta farko da ta ƙaddamar da Tsarin Tafiyar da Makamashi (Energy Transition Plan), kuma ƙasar Afrika ta farko da ta fitar da Dukiyar Ƙasa Kan Daina Amfani da Makamashin Mai (Sovereign Green Bond), sannan ta na cikin ƙasashe na farko da su ka kafa dokar sauyin yanayi ta ƙasa.

“Saboda haka, muka fitar da wannan karin haske game da cece-kucen da ake yi na tafiya da mutane fiye da kima zuwa taron COP28, Shugaba Tinubu da sauran jami’an Gwamnatin Tarayya sun je Dubai ne domin gudanar da aiki tukuru ba sharholiya ba.”

COP28
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
An Bayyana Rawar Da Kasar Sin Ta Taka Kan Sauyin Yanayi Yayin Taron COP28

An Bayyana Rawar Da Kasar Sin Ta Taka Kan Sauyin Yanayi Yayin Taron COP28

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.