• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar ‘Women Link’ Ta Wayar Da Kan Mata Sama Da 200 Kan Zaben 2023

by Abubakar Abba
3 years ago
in Labarai
0
Women link
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gamayyar Kungiyoyin Mata a karkashin inuwar Kungiyar mata da ke fafutukar ganin an samar da shugabanci nagari a kasar nan, wato ‘Women Link For Better Gobernance’, sun yi wa shugabanin kungiyoyin mata bita domin su janyo hankalinsu a kan zaben 2023, mussaman matan Arewacin kasar kan su fito su jefa kuri’un su ga ‘yan takarar da suka cancanta a zabe mai zuwa.

A hirarta da LEADERSHIP Hausa ta yi da Mataimakiyar Shugabar gamayyar kungiyoyin kuma shugabar kungiyar da ke koyar wa mata sana’o’in hannu, Hajiya Aisha Gambo jim kadan bayan kammala taron da ya gudana a Jihar Kaduna ta bayyana cewa, “Makasudin shirya wannan taron shi ne, domin mu wayar wa mata ‘yan’uwanmu kai, musamman matan da ke a arewacin kasar nan, ganin cewa mune a kan gaba wajen fita kwanmu da kwarkwata domin jefa kuri’u a lokacin zabe, amma kuma da an ci zabe sai a barin mu a baya ba tare da an inganta rayuwarmu ba.

  • Kasar Sin Ko Da Yaushe Tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Da Adalci Kan Batun Kasar Ukraine

“Mun wayar wa shugabanin kungiyoyin mata da ke a Jihar Kaduna kai kusan sama da 200, bisa nufin in son koma gida, su ma za su tara sauran ‘ya’yan kungiyoyin mata da suke jagoranta don su wayar masu da kai kan mahimmancin fitowar jefa kuri’un ga ‘yan takarar da suka cancanta lokacin zaben.

“Mata da dama sun yi fishi kan yadda wasu ‘yan siyasar da aka zaba a baya ba su inganta rayuwarsu, inda hakan ya sa matan suka ce sun daina fita jefa kuri’a. Shi ya sa muka hada kai domin mu wayar masu da kai da yi masu nasiha a kan mu yi hakuri mu fito mu jefa kuri’unmu ga ‘yan takarar da suka cancanta.

“Nan ba da dade wa ba, za mu sake wani sabon gangamin wayar da kan ‘yan’uwanmu mata kai wadanda za su fito daga kananan hukumomin 23 da ke a cikin jihar Kaduna kan muhimmancin jefa kuri’a a zaben 2023.”

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Ta kuma yi kira ga iyayen da ke fadin kasar nan da su ja hankalin ‘ya’yansu kar su bari a yi amfani da su don yin bangar siyasa a zaben 2023.

Ita kuwa shugabar gamayyar kungiyar matan, Hajiya Maryan Yahaya Sani wacce kuma ita ce Shugabantar Gidauniyar Ummulkhairi ta ce, “Yanzu mu mata muna son mu hadu mu kafa gwamnati wacce za ta kare martabarmu da kuma ‘ya’yanmu”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

SEMA Ta Raba Wa ‘Yan Gudun Hijira Kayan Abinci A Jihar Borno

Next Post

‘Yan Majalisar Wakilai Sun Bukaci Buhari Ya Yi Kokarin Kubutar Da Mutanan Da Aka Sace

Related

Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

9 hours ago
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja
Labarai

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

10 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

11 hours ago
Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi
Manyan Labarai

Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi

14 hours ago
Zaman lafiya
Labarai

MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025

16 hours ago
Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri
Manyan Labarai

Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

17 hours ago
Next Post
‘Yan Majalisar Wakilai Sun Bukaci Buhari Ya Yi Kokarin Kubutar Da Mutanan Da Aka Sace

'Yan Majalisar Wakilai Sun Bukaci Buhari Ya Yi Kokarin Kubutar Da Mutanan Da Aka Sace

LABARAI MASU NASABA

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

May 29, 2025
An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

May 29, 2025
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

May 29, 2025
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

May 29, 2025
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

May 29, 2025
Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

May 29, 2025
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

May 29, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

May 29, 2025
AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

May 29, 2025
Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

May 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.