ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar ‘Women Link’ Ta Wayar Da Kan Mata Sama Da 200 Kan Zaben 2023

by Abubakar Abba
4 years ago
Women link

Gamayyar Kungiyoyin Mata a karkashin inuwar Kungiyar mata da ke fafutukar ganin an samar da shugabanci nagari a kasar nan, wato ‘Women Link For Better Gobernance’, sun yi wa shugabanin kungiyoyin mata bita domin su janyo hankalinsu a kan zaben 2023, mussaman matan Arewacin kasar kan su fito su jefa kuri’un su ga ‘yan takarar da suka cancanta a zabe mai zuwa.

A hirarta da LEADERSHIP Hausa ta yi da Mataimakiyar Shugabar gamayyar kungiyoyin kuma shugabar kungiyar da ke koyar wa mata sana’o’in hannu, Hajiya Aisha Gambo jim kadan bayan kammala taron da ya gudana a Jihar Kaduna ta bayyana cewa, “Makasudin shirya wannan taron shi ne, domin mu wayar wa mata ‘yan’uwanmu kai, musamman matan da ke a arewacin kasar nan, ganin cewa mune a kan gaba wajen fita kwanmu da kwarkwata domin jefa kuri’u a lokacin zabe, amma kuma da an ci zabe sai a barin mu a baya ba tare da an inganta rayuwarmu ba.

  • Kasar Sin Ko Da Yaushe Tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Da Adalci Kan Batun Kasar Ukraine

“Mun wayar wa shugabanin kungiyoyin mata da ke a Jihar Kaduna kai kusan sama da 200, bisa nufin in son koma gida, su ma za su tara sauran ‘ya’yan kungiyoyin mata da suke jagoranta don su wayar masu da kai kan mahimmancin fitowar jefa kuri’un ga ‘yan takarar da suka cancanta lokacin zaben.

ADVERTISEMENT

“Mata da dama sun yi fishi kan yadda wasu ‘yan siyasar da aka zaba a baya ba su inganta rayuwarsu, inda hakan ya sa matan suka ce sun daina fita jefa kuri’a. Shi ya sa muka hada kai domin mu wayar masu da kai da yi masu nasiha a kan mu yi hakuri mu fito mu jefa kuri’unmu ga ‘yan takarar da suka cancanta.

“Nan ba da dade wa ba, za mu sake wani sabon gangamin wayar da kan ‘yan’uwanmu mata kai wadanda za su fito daga kananan hukumomin 23 da ke a cikin jihar Kaduna kan muhimmancin jefa kuri’a a zaben 2023.”

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ta kuma yi kira ga iyayen da ke fadin kasar nan da su ja hankalin ‘ya’yansu kar su bari a yi amfani da su don yin bangar siyasa a zaben 2023.

Ita kuwa shugabar gamayyar kungiyar matan, Hajiya Maryan Yahaya Sani wacce kuma ita ce Shugabantar Gidauniyar Ummulkhairi ta ce, “Yanzu mu mata muna son mu hadu mu kafa gwamnati wacce za ta kare martabarmu da kuma ‘ya’yanmu”.

Women link
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
‘Yan Majalisar Wakilai Sun Bukaci Buhari Ya Yi Kokarin Kubutar Da Mutanan Da Aka Sace

'Yan Majalisar Wakilai Sun Bukaci Buhari Ya Yi Kokarin Kubutar Da Mutanan Da Aka Sace

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.