• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyoyi Sun Nemi Majalisar Dattawa Ta Sa Baki A Cire Karamin Ministan Tsaro

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Kungiyoyi Sun Nemi Majalisar Dattawa Ta Sa Baki A Cire Karamin Ministan Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata ƙungiya ta gamayyar ƙungiyoyin rajin kare dimokuraɗiyya da haƙƙin dan Adam, CSAGP, sun gudanar da zanga-zanga a hanyar shiga harabar Majalisar Dattawa, inda suke neman a cire Ƙaramin Ministan Tsaro, tsohon gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle.

Masu zanga-zangar na so a cire Matawalle ne  sabida zarginsa da Gwamnatin Zamfara ta yi kan harƙallar “sace kuɗaɗe da batun matsalar ‘yan bindiga a jihar.”

  • Majalisa Ta Soke Bukatar Siyo Jirgin Ruwan Shugaban Kasa, Ta Kara Kudin Ga Lamunin Dalibai
  • Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Da Kafa Kamfanin Abinci Na ‘Arla’

An ga masu zanga-zangar a hanyar zuwa Majalisar Ƙasa dauke da kwalaye da alluna da rubutu akai a ranar Talata, suna kira ga Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ya nusar da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, domin ya tsige Matawalle.

 

Masu zanga-zangar waɗanda ake kiran gamayyar ƙungiyar ta su da suna ‘Civil Society Advocacy Groups and Probity’, sun kuma zargi Minista Matawalle da laifin jawo ‘yan bindiga a jiki, lamarin da suka ce ya haifar da asarar ɗimbin rayuka da dama a Zamfara da asarar dukiyoyi na Biliyoyin Nairori.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Gungun gamayyar ƙungiyar a ƙarƙashin Danesi Momoh, a wani taron manema labarai a ranar Lahadi ya yi kira da a sauke Karamin Ministan Harkokin Tsaron tun a baya.

‘Yan watanni kaɗan kafin saukarsa daga kan kujerar Gwamnatin Zamfara a ranar 29 ga Mayu, EFCC ta zargi Matawalle da karkatar da Naira biliyan 70 na al’ummar jihar, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce tsakaninsa da shugaban EFCC na lokacin, Abdulrasheed Bawa.

Masu zanga-zangar sun damƙa wa Majalisar Dattawa takardar ƙorafi domin isarwa ga Shugaban Majalisar Dattawa, Akpabio, mai ɗauke da zargin cewa, mutum kamar Matawalle ba abin bai wa amanar tsaron ƙasa ba ne, musamman muƙami mai muhimmanci a Ma’aikatar Harkokin Tsaro.

Sun kafa hujjojinsu da dalilansu kan wasu zarge-zargen da Gwamantin Zamfara ta watsa kuma ta wallafa, mai nuni kan yadda Matawalle ya karkatar da Biliyoyin Nairorin Zamfara, a harƙallar kwangiloli daban-daban, ciki har da kwangilar gina filin jirgin saman saukale da lodin kaya a Gusau.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bello MatawalleMa'aikatar tsaroZamafara
ShareTweetSendShare
Previous Post

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cin Zarafin Shugabanta, Ajaero

Next Post

Ministan Wajen Sin Ya Yi Kira Da A Tsagaita Wuta A Gaza

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

7 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

9 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

11 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

14 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

16 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

17 hours ago
Next Post
Ministan Wajen Sin Ya Yi Kira Da A Tsagaita Wuta A Gaza

Ministan Wajen Sin Ya Yi Kira Da A Tsagaita Wuta A Gaza

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.