• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kurar Da Ta Biyo Bayan Janye Yajin Aiki

byYusuf Shuaibu
2 years ago
Aiki

A wannan makon ne gamayyar kungiyoyin kwadago (NLC) da kungiyar kasuwanci (TUC) suka janye shirinsu na tsunduma yajin aikin sai baba ta gani daga da suka shirya za su yi.

Wannan matakin janyewar ya zo ne, bayan wata doguwar tattaunawa tsakanin wakilan kungiyoyin da wakilan gwamnatin tarayya, yanzu dai bangarorin biyun sun cimma matsaya wadda ta kai da dakatar da tsunduma yajin aikin da kwana 30 masu zuwa.

  • Kwamishinan Benue Ya Kubuta Bayan Sace Shi Da Kwana 10
  • Takardun Karatun Tinubu Ba Na Bogi Ba Ne – Fadar Shugaban Kasa

Idan za a iya tunawa kungiyoyin sun yi shirin shiga yajin aikin ne saboda matsin rayuwa da mafi yawan ‘yan Nijeriya suke ciki, wadanda suka samo asali sakamakon cire tallafin man fetur da wasu sabbin manufofi da gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu take aiwatar da su.

Wasu daga cikin abubuwan da aka cimma akwai karin albashi na naira 35,000 da gwamnatin tarayya ta amince za ta bayar ga dukkanin ma’aikatanta, wanda za a fara daga watan Satumbar da ya gabata, kafin a samu matsaya kan sabon mafi karancin albashi wanda ake tsammanin za a mayar da shi doka.

Sannan kuma gwamnatin tarayya ta dakatar da karbar harajin kan man dizel nan da wata shida masu zuwa. Haka kuma akwai maganar motocin sufuri masu amfani da gas da ake sa ran gwamnatin za ta kawo nan ba da jimawa ba don a sami sauyi daga amfani da man fetur.

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

Batun biyan albashin malaman gaba da sakandire na gwamnatin tarayya da ke bin bashi, wanda shi ma an mika shi gaban ma’aikatar kwadago da ayyukan yi domin ci gaba da duba shi.

“Sanya naira biliyan 100 don sayo manyan motocin bas-bas masu amfani da man gas don saukaka wa jama’a kan hanyar zirga-zirga a duk fadin kasar nan, wanda ake sa ran za a yi a watan Nuwamba mai zuwa.

Sannan kuma an cimma yarjejeniyar cire haraji ga wasu kamfanoni da daidaikun jama’a don saukaka masu wajen hada-hadar yau da kullum.

Bugu da kari, an cimma yarjejeniyar sasantawa da kungiyar direbobi ta kasa (NURTW) tare da sanya baki a batun fara biyan naira 25,000 a duk wata daga Oktoba ga ‘yan Nijeriya mutum miliyan15, wanda ya hada da tsofaffin ma’aikata masu karbar fansho.

Akwai kuma kara fadada shirin nan na rabon taki ga manoma a duk fadin kasar nan. Haka kuma an amince da cewa su ma jihohi da kananan hukumomi za a karfafa masu gwiwa domin aiwatar da wannan karin albashi ga ma’aikatan su.

Za a samar da kudade ga matsakaita da kananan masana’antu, sannan za a mayar da hankali wajen kirkiro da ayyuka ga matasa. Sannan kuma a fito da shirin zagaya matatun man fetur din kasar nan don tantance irin gyaran da suke bukata.

Wani abu kuma shi ne, gwamnatin tarayya za ta yi amfani da takardun da kotu ta sahale ne wajen saka hannu a kan wannan yarjejeniyar fahimtar juna cikin mako daya.

Ita dai wannan yarjejeniya ta samu sanya hannun shugaban kungiyar NLC, Joe Ajaero da sakataren kungiyar, Emmanuel Ugboaja da shugaban kungiyar TUC, Festus Osifo da sakataren kungiyar, Nuhu A. Toro

A bangaren gwamnatin tarayya kuwa, akwai ministan kwadago, Simon Bako Lalong da karamin ministansa, Nkeiruka Onyejeocha da kuma ministan yada labarai, Alhaji Mohammed Idris.

Wannan lamari na yajin aikin kungiyar kwadago ya tayar da kura a cikin kasar nan, wanda ‘yan Nijeriya suke ta bayyana ra’ayoyinsu kan lamarin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Next Post
Matsayin Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Na Zuba Dagwalon Nukiliya A Cikin Teku Bai Sauya Ba

Matsayin Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Na Zuba Dagwalon Nukiliya A Cikin Teku Bai Sauya Ba

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version