ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kurar Da Ta Biyo Bayan Janye Yajin Aiki

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Aiki

A wannan makon ne gamayyar kungiyoyin kwadago (NLC) da kungiyar kasuwanci (TUC) suka janye shirinsu na tsunduma yajin aikin sai baba ta gani daga da suka shirya za su yi.

Wannan matakin janyewar ya zo ne, bayan wata doguwar tattaunawa tsakanin wakilan kungiyoyin da wakilan gwamnatin tarayya, yanzu dai bangarorin biyun sun cimma matsaya wadda ta kai da dakatar da tsunduma yajin aikin da kwana 30 masu zuwa.

  • Kwamishinan Benue Ya Kubuta Bayan Sace Shi Da Kwana 10
  • Takardun Karatun Tinubu Ba Na Bogi Ba Ne – Fadar Shugaban Kasa

Idan za a iya tunawa kungiyoyin sun yi shirin shiga yajin aikin ne saboda matsin rayuwa da mafi yawan ‘yan Nijeriya suke ciki, wadanda suka samo asali sakamakon cire tallafin man fetur da wasu sabbin manufofi da gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu take aiwatar da su.

ADVERTISEMENT

Wasu daga cikin abubuwan da aka cimma akwai karin albashi na naira 35,000 da gwamnatin tarayya ta amince za ta bayar ga dukkanin ma’aikatanta, wanda za a fara daga watan Satumbar da ya gabata, kafin a samu matsaya kan sabon mafi karancin albashi wanda ake tsammanin za a mayar da shi doka.

Sannan kuma gwamnatin tarayya ta dakatar da karbar harajin kan man dizel nan da wata shida masu zuwa. Haka kuma akwai maganar motocin sufuri masu amfani da gas da ake sa ran gwamnatin za ta kawo nan ba da jimawa ba don a sami sauyi daga amfani da man fetur.

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Batun biyan albashin malaman gaba da sakandire na gwamnatin tarayya da ke bin bashi, wanda shi ma an mika shi gaban ma’aikatar kwadago da ayyukan yi domin ci gaba da duba shi.

“Sanya naira biliyan 100 don sayo manyan motocin bas-bas masu amfani da man gas don saukaka wa jama’a kan hanyar zirga-zirga a duk fadin kasar nan, wanda ake sa ran za a yi a watan Nuwamba mai zuwa.

Sannan kuma an cimma yarjejeniyar cire haraji ga wasu kamfanoni da daidaikun jama’a don saukaka masu wajen hada-hadar yau da kullum.

Bugu da kari, an cimma yarjejeniyar sasantawa da kungiyar direbobi ta kasa (NURTW) tare da sanya baki a batun fara biyan naira 25,000 a duk wata daga Oktoba ga ‘yan Nijeriya mutum miliyan15, wanda ya hada da tsofaffin ma’aikata masu karbar fansho.

Akwai kuma kara fadada shirin nan na rabon taki ga manoma a duk fadin kasar nan. Haka kuma an amince da cewa su ma jihohi da kananan hukumomi za a karfafa masu gwiwa domin aiwatar da wannan karin albashi ga ma’aikatan su.

Za a samar da kudade ga matsakaita da kananan masana’antu, sannan za a mayar da hankali wajen kirkiro da ayyuka ga matasa. Sannan kuma a fito da shirin zagaya matatun man fetur din kasar nan don tantance irin gyaran da suke bukata.

Wani abu kuma shi ne, gwamnatin tarayya za ta yi amfani da takardun da kotu ta sahale ne wajen saka hannu a kan wannan yarjejeniyar fahimtar juna cikin mako daya.

Ita dai wannan yarjejeniya ta samu sanya hannun shugaban kungiyar NLC, Joe Ajaero da sakataren kungiyar, Emmanuel Ugboaja da shugaban kungiyar TUC, Festus Osifo da sakataren kungiyar, Nuhu A. Toro

A bangaren gwamnatin tarayya kuwa, akwai ministan kwadago, Simon Bako Lalong da karamin ministansa, Nkeiruka Onyejeocha da kuma ministan yada labarai, Alhaji Mohammed Idris.

Wannan lamari na yajin aikin kungiyar kwadago ya tayar da kura a cikin kasar nan, wanda ‘yan Nijeriya suke ta bayyana ra’ayoyinsu kan lamarin.

Aiki
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Next Post
Matsayin Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Na Zuba Dagwalon Nukiliya A Cikin Teku Bai Sauya Ba

Matsayin Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Na Zuba Dagwalon Nukiliya A Cikin Teku Bai Sauya Ba

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.